Hausa translation of the meaning Page No 379

Quran in Hausa Language - Page no 379 379

Suratul Al-Naml from 23 to 35


23. « Lalle ni nã sãmi wata mace wadda tanã mulkinsu kuma an bã ta daga dukkan kõme, kuma tanã da gadon sarauta mai girma. »
24. « Na sãme ta ita da mutãnenta, sunã yin sujada ga rãnã, baicin Allah, kuma Shaiɗan ya ƙawãce musu ayyukansu, sabõda haka ya karkatar da su daga hanya, sa'an nan sũ, ba su shiryuwa. »
25. « Ga ( 1 ) su yi sujada ga Allah Wanda Yake fitar da abin da yake a ɓõye, a cikin sammai da ƙasa, kuma Yã san abin da kuke ɓõyẽwada abin da kuke bayyanãwa. »
26. « Allah bãbu abin bautãwa fãce shĩ Ubangijin ( 2 ) Al'arshi, mai girma. »
27. Ya ce: « Za mu dũba shin kã yi gaskiya ne, kõ kuwa kã kasance daga maƙaryata? »
28. « Ka tafi da takardata wannan, sa'an nan ka jẽfa ta zuwa gare su, sa'an nan kuma ka jũya daga barinsu, sa'an nan ka ga mẽne ne suke mayarwa. »
29. Ta ce: « Yã kũ mashawarta! Lalle ne, an jẽfo, zuwa gareni, wata takarda mai girma. »
30. « Lalle ita daga Sulaiman take, kuma lalle ita da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai ne. »
31. « Kada ku yi girman kai a gare ni, kuma ku zo mini kunã mãsu sallamãwa. »
32. Ta ce: « Yã ku mashawarta ( 3 ) ! Ku yi Mini fatawa ga al'amarĩna, ban kasance mai yanke wani al'amari ba, sai kun halarta. »
33. Suka ce: « Mũ ma'abũta ƙarfi ne, kuma ma'abbũta yãƙi mai tsanani ne, kuma al'amari yã kõma zuwa gare ki, sabõda haka ki dũbamẽne ne zã ki yi umurui ( da shi ) ? »
34. Ta ce: « Lalle sarakuna idan sun shiga wata alƙarya, sai su ɓãta ta, kuma su sanya mãsu darajar mutãnenta ƙasƙantattu. Kuma kamar wancan ne suke likatãwa. »
35. « Kuma lalle nĩ mai aikãwa ce zuwa gare su da kyauta, sa'an nan mai dũbawa ce: Da me manzannin zã su kõmo. »
( 1 ) An kãyar da harafin kõrewa dõmin barinsa, da Hausa, yanã ɓãta ma'ana, dõmin shaiɗan bai kange su daga rashin yin sujada ba.
( 2 ) Ya siffanta Allah da cẽwa bãbu abin bautãwa fãce Shi, dõmin ya kõre cancantar rãnã ga ibãda, da Ubangijin Al'arshi dõmin ya ɗẽbe girman gadon Bilkisu daga zukãta.
( 3 ) Allah bai kẽɓance hikima ga maza kawai ba har mãtã akwai mãsu hikima a cikinsu. Sai dai Musulunci yã hana shugabancin mãtã, sabõda galibinsu ãdifarsu tã rinjãyi hankalinsu, sabõda kyautata tarbiyyar yãra. Anã fahimtar cẽwa iya mulki shi ne rashin fallẽwa da ra'ayi ga shũgaba, sai a bãyan ya shãwarci mutãnensa, kamar yadda sarauniyar Saba' ta yi da Majalisarta.