Hausa translation of the meaning Page No 139

Quran in Hausa Language - Page no 139 139

Suratul Al-An'am from 91 to 94


91. Kuma ba su ƙaddara Allah a kan hakkin ƙaddara shi ba, a lõkacin da suka ce: « Allah bai saukar da kõme ba ga wani mutum. » Ka ce: « Wãne ne ya saukar da Littãfi wanda Mũsã ya zo da shi, yanã haske da shiriya ga mutãne, kunã sanya shi takardu, kũna bayyana su, kuma kunã ɓõye mai yawa, kuma an sanar da ku abin da ba ku sani ba, ku da ubanninku? » Ka ce: « Allah, » ( 1 ) sa'an nan ka bar su a cikin sharhõliyarsu sunã wãsã.
92. Kuma wannan Littãfi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, mai gaskata wanda yake a gabansa ne, kuma dõmin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu ( Makka ) da wanda yake gefenta. Kuma waɗanda suke yin ĩmãni da Lãhira sunã ĩmãni da shi ( Alƙur'ãni ) , kuma sũ, a kan sallarsu, sunã tsarẽwa.
93. Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ce: « An yi wahayi zuwa gare ni, » alhãli kuwa ba a yi wahayin kõme ba zuwa gare shi, da wanda ya ce: « zan saukar da misãlin abin da Allah Ya saukar? » Kuma dã kã gani, a lõkacin da azzãlumai suke cikin mãyen mutuwa, kuma malã'iku sunã mãsu shimfiɗa hannuwansu, ( sunã ce musu ) « Ku fitar da kanku; a yau anã sãka muku da azãbar wulãƙanci sabõda abin da kuka kasance kunã faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma kun kasance daga ãyõyinSa kunã yin girman kai. »
94. Kuma lalle ne haƙĩƙa, kun zo Mana ɗai ɗai, kamar yadda Muka halittã ku a farkon lõkaci. Kuma kun bar abin da Muka mallaka muku a bayan bayayyakinku, kuma ba Mu gani a tãre da kũ ba, macẽtanku waɗanda kuka riya cẽwa lalle ne sũ, a cikinku mãsu tãrayya ne. Lalle ne, hãƙĩƙa,kõme yã yanyanke a tsakãninku, kuma abin da kuka kasance kunã riyãwa ya ɓace daga gare ku.
( 1 ) Allah ne Ya saukar da shi, sabõda haka ba zai zama abin mãmãki ba ko abin musu ga Ya saukar da wani littãfi kamar Alƙur'ãni ga wani mutum a bãyan Taurãta ga Musã. Kuma a cikin Taurãtar ba a ce ita ce ƙarshen Littãfin Allah ba kuma Mũsã bã shi ne ƙarshen Annabawa ba.