Hausa translation of the meaning Page No 381

Quran in Hausa Language - Page no 381 381

Suratul Al-Naml from 45 to 55


45. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, mun aika zuwa Samũdãwa da ɗan'uwansu, Salihu ( ya ce ) , « Ku bauta wa Allah. » Sai gã su ƙungiyõyi biyu sunã ta husũma.
46. Ya ce: « Yã mutãnẽna! Don me kuke nẽman gaggãwa game da mũnanãwa, a gabãnin kyautatãwa. Don me bã ku nẽman Allah gãfara, tsammãninku, zã a yi muku rahama? »
47. Suka ce: « Munã shu'umci da kai, kuma da wanda ke tãre da kai. » Ya ce: « Shu'umcinku a wurin Allah yake. Ã'a, kũ mutãne ne, anã fitinar ku. »
48. Kuma waɗansu jama'a tara ( 1 ) sun kasance a cikin birnin, sunã yin ɓarna, kuma bã su kyautatãwa. Suka ce: « Ku yi rantsuwa da Allah, lalle zã mu kwãnan masa, ( 2 ) shi da mutãnensa sa'an nan mu ce wa waliyyinsa. 'Ba mu halarci halakar mutãnensa ba kuma mũ, haƙĩ ƙa, mãsu gaskiya ne'. »
50. Kuma suka ƙulla mãkirci, kuma Muka ƙulla sakamakon mãkirci, alhãli sũ ba su sani ba.
51. Ka dũba yadda ãƙibar mãkircinsu ta kasance lalle Mũ Mun darkãke su da mutãnensu, gabã ɗaya.
52. Waɗancan, gidãjensu ne, wõfintattu sabõda zãluncin da suka yi, lalle ne a wancan akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke sani.
53. Muka tsĩrar da waɗanda suka yi ĩmãni, kuma sun kasance sunã taƙawa.
54. Da Lũdu, a lõkacin da ya ce wa mutãnensa, « Shin kunã jẽ wa alfasha ( 3 ) ne, alhãli, kuwa kunã gani? »
55. « Shin lalle kũ haƙĩƙa kunã je wa maza da sha'awa baicin mãtã? Ã'a, kũ wasu irin mutãne ne kuna aikin jãhilci. »
( 1 ) Yawan mãsu ɓarnã bã ya hana gaskiya bayyana. Kuma mai mãkirci dõmin ya halakar da mai gargaɗin addinin Allah, yanã yi wa kansa sanadin halaka kawai ne. Waɗannan mutãne tara sun yi niyyar kashe Sãlihu ne, bã da sanin danginsa ba, a wurin dayake kwãna yanã salla a masallacinsa, a bãyan gari. A can Allah ya halakar da su. Wannan shĩ ne sakamakon mãkircin da suka ƙulla.
49.
( 2 ) Zã mu kwãnan masa, ai zãmu kwãna da niyyar kashe shi a cikin dare, a ɓõye.
( 3 ) Alfãshar mutãnen Lũɗu, ita ce luwãɗi, namji yabi namiji a duburarsa wannan alfãsha, kõ dabbõbi bã su yin ta. Ga mutãnen Lũɗuta fãra bayyana. Allah Ya halakar da su kamar yadda Ya ambata. Sa'an nan kuma ba a ƙãra ganinta ba, sai ga wannan al'umma asĩirin da ke ciki, shĩ ne yadda Allah Yake jũyar da ɗabĩ'ar mutum ta zama bã ta mãsu hankali ba, tãre da dõgewar halittar jikinsa kamar yadda take ga zãhiri.