Hausa translation of the meaning Page No 325

Quran in Hausa Language - Page no 325 325

Suratul Al-Anbiya from 36 to 44


36. Kuma idan waɗanda suka kãfirta suka gan ka, bã su riƙon ka fãce da izgili ( sunã cẽwa ) , « Shin, wannan ne ke ambatar gumãkanku? » Alhãli kuwa sũ, ga ambatar Mai rahama, mãsu kãfirta ( 1 ) ne.
37. An halitta mutum daga gaggãwa, zan nũna muku ãyõyiNa. Sabõda haka kada ku nẽmiyin gaggãwa.
38. Kuma sunã cẽwa, « A yaushe wannan wa'adi zai tabbata, idan kun kasance mãsu gaskiya? »
39. Dã waɗanda suka kãfirta sunã sanin lõkacin da bã su kange wuta daga fuskõkinsu, kuma haka daga bãyayyakinsu, alhãli kuwa ba su zama ana taimakon su ba.
40. Ã'a, tanã jẽ musu bisa ga auke sai ta ɗimautar da su, sa'an nan bã su iya mayar da ita, kuma ba su zama anã yi musu jinkiri ba.
41. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili ga waɗansu Manzanni daga gabãninka, sai abin da suka kasance sunã izgili da shi ya auku ga waɗanda suka yi izgilin daga gare su.
42. Ka ce: « Wãne ne yake tsare ku a dare da yini daga Mai rahama? » Ã'a, sũ mãsu bijirẽwa ne daga ambaton Ubangijinsu.
43. Ko kuwa sunã da waɗansu abũbuwan bautãwa waɗanda ke tsare su, daga gare Mu? Bã su iya taimakon kansu kuma ba su kasance anã abũtar su ( 2 ) ba daga gareMu.
44. Ã'a, Mun yalwata wa waɗannan da ubanninsu ni'imarMu, har rãyuwa ta yi tsawo a kansu. Shin, to, bã su ganin cẽwa lalle Mũ, Munã je wa ƙasarsu, Munã rage ( 3 ) ta daga sãsanninta? Shin, to, su ne marinjaya?
( 1 ) Sun kasance sunã aibanta wanda yake musun gumãkansu alhãli kuwa sũ, sunã musun zaman Allah Mai rahama ya kasance abin bautãwa guda. Wannan shi ne gãyar jãhilci.
( 2 ) Bã su iya sãmun wani abõkiwanda zai tsare su daga azãbarMu. Kuma wanda bai tsarekansa ba yãya zaĩ iya tsare wani?
( 3 ) Munã rage ƙasarsu daga sãsanninta, watau mutãnen da ke bin su ga ɓatarsu kullum sunã raguwa, sunã shiga Musulunci, Musulunci na ƙãruwa.