📖 0/604 shafuka an karanta
📄 564
فَلَمَّا رَأَوۡهُ زُلۡفَةً سِيٓـَٔتۡ وُجُوهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَقِيلَ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَدَّعُونَ  ۝٢٧ قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَهۡلَكَنِيَ ٱللَّهُ وَمَن مَّعِيَ أَوۡ رَحِمَنَا فَمَن يُجِيرُ ٱلۡكَٰفِرِينَ مِنۡ عَذَابٍ أَلِيمٍ  ۝٢٨ قُلۡ هُوَ ٱلرَّحۡمَٰنُ ءَامَنَّا بِهِۦ وَعَلَيۡهِ تَوَكَّلۡنَاۖ فَسَتَعۡلَمُونَ مَنۡ هُوَ فِي ضَلَٰلٍ مُّبِينٍ  ۝٢٩ قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَصۡبَحَ مَآؤُكُمۡ غَوۡرًا فَمَن يَأۡتِيكُم بِمَآءٍ مَّعِينِۭ  ۝٣٠
Surah Al-Qalam
bismillah
نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ  ۝١ مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٍ  ۝٢ وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٍ  ۝٣ وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ  ۝٤ فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ  ۝٥ بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ  ۝٦ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ  ۝٧ فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ  ۝٨ وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ  ۝٩ وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ  ۝١٠ هَمَّازٍ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٍ  ۝١١ مَّنَّاعٍ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ  ۝١٢ عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ  ۝١٣ أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ  ۝١٤ إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ  ۝١٥
67:27
فَلَمَّا رَأَوۡهُ زُلۡفَةً سِيٓـَٔتۡ وُجُوهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَقِيلَ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَدَّعُونَ  ۝٢٧
To, lokacin da suka gan ta (azãbar) a kusa, fuskokin waɗanda suka kãfirta suka mũnana, kuma aka ce (musu) wannan shi ne abin da kuka zamo kuna ƙaryatãwa.
67:28
قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَهۡلَكَنِيَ ٱللَّهُ وَمَن مَّعِيَ أَوۡ رَحِمَنَا فَمَن يُجِيرُ ٱلۡكَٰفِرِينَ مِنۡ عَذَابٍ أَلِيمٍ  ۝٢٨
Ka ce musu "Idan Allah Ya halaka ni nĩ da wanda ke tãre da ni, ko kuma, Yã yi mana rahama, to, wãne ne zai tserar da kafirai daga wata azãba mai raɗaɗi?"
67:29
قُلۡ هُوَ ٱلرَّحۡمَٰنُ ءَامَنَّا بِهِۦ وَعَلَيۡهِ تَوَكَّلۡنَاۖ فَسَتَعۡلَمُونَ مَنۡ هُوَ فِي ضَلَٰلٍ مُّبِينٍ  ۝٢٩
Ka ce: "Shĩ ne Mai rahama mun yi ĩmãni da Shi, gare Shi muka dogara, saboda haka zã ku san wanda yake a cikin ɓata bayyananniya."
67:30
قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَصۡبَحَ مَآؤُكُمۡ غَوۡرًا فَمَن يَأۡتِيكُم بِمَآءٍ مَّعِينِۭ  ۝٣٠
Ka ce: "Ko kun gani, idan ruwanku ya wãyi gari faƙaƙƙe, to, wãne ne zai zo muku da ruwa wani mai ɓuɓɓuga?"
Surah Al-Qalam
bismillah
68:1
نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ  ۝١
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
68:2
مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٍ  ۝٢
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
68:3
وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٍ  ۝٣
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
68:4
وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ  ۝٤
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
68:5
فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ  ۝٥
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
68:6
بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ  ۝٦
Ga wanenku haukã take.
68:7
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ  ۝٧
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
68:8
فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ  ۝٨
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
68:9
وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ  ۝٩
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
68:10
وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ  ۝١٠
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
68:11
هَمَّازٍ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٍ  ۝١١
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
68:12
مَّنَّاعٍ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ  ۝١٢
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
68:13
عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ  ۝١٣
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
68:14
أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ  ۝١٤
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
68:15
إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ  ۝١٥
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."


📚Juz 29 📄564 / 604



Mishary Rashid Alafasy
Mahmoud Khalil Al-Husary
Abdurrahman As-Sudais
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
Abdul Basit Abdul Samad
Ali Al-Hudhaify
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
Abu Bakr Ash-Shaatree
Muhammad Ayyoub
Abdullah Basfar
Abdullah Al-Juhani
Maher Al Muaiqly
0:00
0:00
-

Al-Kur'ani


Monday, August 31, 2026

Don't forget us in your sincere prayers