📖 0/604 shafuka an karanta
📄 584
إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى  ۝١٦ ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ  ۝١٧ فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ  ۝١٨ وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ  ۝١٩ فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ  ۝٢٠ فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ  ۝٢١ ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ  ۝٢٢ فَحَشَرَ فَنَادَىٰ  ۝٢٣ فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ  ۝٢٤ فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ  ۝٢٥ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةً لِّمَن يَخۡشَىٰٓ  ۝٢٦ ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا  ۝٢٧ رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا  ۝٢٨ وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا  ۝٢٩ وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ  ۝٣٠ أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا  ۝٣١ وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا  ۝٣٢ مَتَٰعًا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ  ۝٣٣ فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ  ۝٣٤ يَوۡمَ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ  ۝٣٥ وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ  ۝٣٦ فَأَمَّا مَن طَغَىٰ  ۝٣٧ وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا  ۝٣٨ فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ  ۝٣٩ وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ  ۝٤٠ فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ  ۝٤١ يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا  ۝٤٢ فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ  ۝٤٣ إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ  ۝٤٤ إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا  ۝٤٥ كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا  ۝٤٦
79:16
إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى  ۝١٦
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
79:17
ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ  ۝١٧
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
79:18
فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ  ۝١٨
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
79:19
وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ  ۝١٩
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
79:20
فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ  ۝٢٠
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
79:21
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ  ۝٢١
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
79:22
ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ  ۝٢٢
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
79:23
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ  ۝٢٣
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
79:24
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ  ۝٢٤
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
79:25
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ  ۝٢٥
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
79:26
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةً لِّمَن يَخۡشَىٰٓ  ۝٢٦
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
79:27
ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا  ۝٢٧
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
79:28
رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا  ۝٢٨
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
79:29
وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا  ۝٢٩
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
79:30
وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ  ۝٣٠
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
79:31
أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا  ۝٣١
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
79:32
وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا  ۝٣٢
Da duwatsu, Yã kafe ta.
79:33
مَتَٰعًا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ  ۝٣٣
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
79:34
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ  ۝٣٤
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
79:35
يَوۡمَ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ  ۝٣٥
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
79:36
وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ  ۝٣٦
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
79:37
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ  ۝٣٧
To, amma wanda ya yi girman kai.
79:38
وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا  ۝٣٨
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
79:39
فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ  ۝٣٩
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
79:40
وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ  ۝٤٠
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
79:41
فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ  ۝٤١
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
79:42
يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا  ۝٤٢
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
79:43
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ  ۝٤٣
Me ya haɗã ka da ambatonta?
79:44
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ  ۝٤٤
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
79:45
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا  ۝٤٥
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
79:46
كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا  ۝٤٦
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.


📚Juz 30 📄584 / 604



Mishary Rashid Alafasy
Mahmoud Khalil Al-Husary
Abdurrahman As-Sudais
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
Abdul Basit Abdul Samad
Ali Al-Hudhaify
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
Abu Bakr Ash-Shaatree
Muhammad Ayyoub
Abdullah Basfar
Abdullah Al-Juhani
Maher Al Muaiqly
0:00
0:00
-

Al-Kur'ani


Tuesday, September 1, 2026

Don't forget us in your sincere prayers