Surah Nuh
PDF —
Built right in your browser — download starts automatically
Surah Nuh pdf — Sauke (Hausa)
Surah Nuh pdf Hausa — Sauke Surah Nuh Fassara. Nuh (Meccan) 28 Aya.
Related
- Nuh FassaraHausa
- Nuh mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah Nuh

ﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆ
Lalle ne Mun aiki Nũhu zuwa ga mutãnensa, cẽwa ka yi gargaɗi ga mutãnenka gabãnin wata azãba mai raɗaɗi ta zo musu.
ﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍ
Ya ce: "Ya mutãnena ni, a gare ku, mai gargaɗi ne, mai bayyanãwa."
ﮎﮏﮐﮑﮒﮓ
"Cewa ku bauta wa Allah, ku ji tsõronSa, kuma ku bĩ ni."
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨ
"Allah zai gãfarta muku daga zunubanku kuma Ya jinkirta muku zuwa ga ajalin da aka ambata. Lalle ne ajalin Allah idan ya zo, ba za a jinkirta Shi ba, dã kun kasance masana (ga abin da nake faɗã dã, kun bar kãfirci)."
ﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰ
Nũhu) ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne, na kirãyi mutãnena, a cikin dare da yini."
ﮱﯓﯔﯕﯖﯗ
"To, amma kirana bai ƙãre su ba sai da, gudu (daga gare ni)."
ﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
"Kuma lalle ne ni, kõ da yaushe na kirãye su dõmin Ka gãfarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufãfinsu, su dõge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyãkar girman kai."
ﯧﯨﯩﯪﯫ
"Sa'an nan lalle ne ni, na kira su, a bayyane."
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳ
"Sa'an nan lalle ne, na yi yẽkuwa sabõda su, kuma na gãna da su a cikin asĩri."
ﯴﯵﯶﯷﯸﯹﯺ
"Shi na ce, 'Ku nẽmi gãfara daga Ubangijinku, lalle ne shi Ya kasance Mai gãfara ne."
ﭑﭒﭓﭔﭕ
"Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga."
ﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟ
"Kuma ya yalwata muku game da dũkiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gõnaki, kuma Ya sanya muku koguna."
ﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
"Me ya sãme ku, bã ku fãtar sãmun natsuwa daga Allah,"
ﭧﭨﭩﭪ
"Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye?"
ﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
"Ba ku ga yadda Allah Ya halitta wasu sammai bakwai ɗabaƙõƙĩ a kan jũna ba?"
ﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻ
"Ya sanya watã a cikinsu, yana mai haske, Ya sanya rãnã babbar fitila?"
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
"Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa."
ﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
"Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa."
ﮈﮉﮊﮋﮌﮍ
"Kuma Allah Ya sanya muku ƙasa shimfidaɗɗiya."
ﮎﮏﮐﮑﮒ
"Dõmin ku shiga a cikinta, hanyõyi mãsu fãɗi."
ﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
Nũhu ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne sũ sun saɓa mini sun bi wanda dukiyarsa da ɗiyansa ba su ƙãre shi da kõme ba sai da hasãra."
ﮡﮢﮣﮤ
"Kuma sun yi wani mãkirci, mãkirci babba."
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
"Kuma suka ce: Faufau kada ku bar gumãkanku, kuma faufau, kada ku bar wadda, kuma kada ku bar suwã kuma kada ku bar Yagũsa da Ya'ũƙa da Nasra."
ﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝ
"Kuma lalle ne sun ɓatar da (mutãne) mãsu yawa, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai (kõme) sai ɓata."
ﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪ
Sabõda laifukansu na ganganci aka nutsar da su, sa'an nan aka sanya su a wuta. Saboda haka ba su sãmã wa kansu wani mataimaki wanin Allah ba.
ﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
Kuma Nũhu ya ce: "Ya Ublngijina! Kada Ka bari, a kan ƙasa, daga cikin kãfirai, wanda ke zama a cikin gida."
ﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀ
"Lalle ne, Kai idan Ka bar su, zã su ɓatar da bãyinKa, kuma bã zã su haifi kowa ba fãce fãjiri mai yawan kãfirci"
ﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑ
"Ya Ubanginjina! Ka yi mini gãfara (ni) da mahaifana biyu, da wanda ya shiga gidana, yana mai ĩmãni, da mũminai maza da mũminai mãtã, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai kõme sai halaka."
Al-Kur'ani
Tuesday, August 18, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







