Surah Al-Hijr
PDF —
Built right in your browser — download starts automatically
Surah Al-Hijr pdf — Sauke (Hausa)
Surah Al-Hijr pdf Hausa — Sauke Surah Al-Hijr Fassara. Al-Hijr (Meccan) 99 Aya.
Related
- Al-Hijr FassaraHausa
- Al-Hijr mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah Al-Hijr

ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘ
A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
ﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
ﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩ
Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃ
Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
ﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌ
"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
ﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞ
Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
ﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
ﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯ
Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
ﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
ﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞ
Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨ
Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
ﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱ
Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
ﭙﭚﭛﭜﭝﭞ
Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
ﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
ﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻ
Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
ﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛ
Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
ﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞ
Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫ
Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
ﯶﯷﯸﯹﯺ
Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
ﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂ
Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙ
Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
ﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥ
Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫ
Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
ﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
"Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹ
Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
ﭺﭻﭼﭽﭾ
Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
ﭿﮀﮁﮂﮃ
"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
ﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
ﮏﮐﮑﮒﮓ
"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥ
"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
ﮦﮧﮨﮩﮪ
Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
ﯕﯖﯗﯘﯙﯚ
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
ﯛﯜﯝﯞ
"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲ
Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
ﯳﯴﯵﯶﯷﯸﯹﯺ
Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
ﯻﯼﯽﯾﯿﰀ
Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
ﰁﰂﰃﰄﰅ
Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚ
A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
ﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢ
Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫ
Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
ﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
ﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼ
Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
ﭽﭾﭿﮀﮁﮂ
Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉ
Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐ
"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗ
"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝ
To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
ﮞﮟﮠﮡﮢ
Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
ﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
ﮫﮬﮭﮮﮯ
"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
ﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟ
"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
ﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
ﯪﯫﯬﯭﯮ
Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
ﯶﯷﯸﯹﯺ
"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
ﯻﯼﯽﯾﯿﰀ
Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗ
Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
ﭞﭟﭠﭡ
Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
ﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪ
Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
ﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
ﭱﭲﭳﭴ
Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
ﮁﮂﮃﮄﮅﮆ
Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
ﮇﮈﮉﮊﮋﮌ
Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
ﮍﮎﮏﮐﮑﮒ
Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
ﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
ﮚﮛﮜﮝ
Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
ﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤ
Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
ﯗﯘﯙﯚﯛﯜ
Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
ﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.
ﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
ﯵﯶﯷﯸﯹﯺ
Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
ﯻﯼﯽﯾﯿ
Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
ﭑﭒﭓﭔﭕ
Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
ﭖﭗﭘﭙ
To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
ﭚﭛﭜﭝ
Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤ
Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
ﭥﭦﭧﭨ
Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
ﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.
Al-Kur'ani
Tuesday, August 18, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







