Al-Fath · 29/29
Fassara Rubutun sauti — Surah Al-Fath
مُّحَمَّدٌ رَّسُولُ اللَّهِ ۚ وَالَّذِينَ مَعَهُ أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَمَاءُ بَيْنَهُمْ ۖ تَرَاهُمْ رُكَّعًا سُجَّدًا يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِّنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا ۖ سِيمَاهُمْ فِي وُجُوهِهِم مِّنْ أَثَرِ السُّجُودِ ۚ ذَٰلِكَ مَثَلُهُمْ فِي التَّوْرَاةِ ۚ وَمَثَلُهُمْ فِي الْإِنجِيلِ كَزَرْعٍ أَخْرَجَ شَطْأَهُ فَآزَرَهُ فَاسْتَغْلَظَ فَاسْتَوَىٰ عَلَىٰ سُوقِهِ يُعْجِبُ الزُّرَّاعَ لِيَغِيظَ بِهِمُ الْكُفَّارَ ۗ وَعَدَ اللَّهُ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ مِنْهُم مَّغْفِرَةً وَأَجْرًا عَظِيمًا ۝٢٩
Muhammadur Rasoolul laah; wallazeena ma`ahooo ashiddaaa`u `alal kuffaaari ruhamaaa`u bainahum taraahum rukka`an sujjadany yabtaghoona fadlam minal laahi wa ridwaanan seemaahum fee wujoohihim min asaris sujood; zaalika masaluhum fit tawraah; wa masaluhum fil Injeeli kazar`in akhraja shat `ahoo fa `aazarahoo fastaghlaza fastawaa `alaa sooqihee yu`jibuz zurraa`a liyagheeza bihimul kuffaar; wa`adal laahul lazeena aamanoo wa `amilus saalihaati minhum maghfiratanw wa ajran `azeemaa
📖 Da Hausa
Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tãre da shi mãsu tsanani ne a kan kãfirai, mãsu rahama ne a tsakãninsu, kanã ganin su sunã mãsu rukũ'i mãsu sujada, sunã nẽman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alãmarsu tanã a cikin fuskõkinsu, daga kufan sujuda. Wannan shĩ ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injĩla ita ce kamar tsiron shũka wanda ya fitar da rẽshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafãfunsa, yanã bãyar da sha'awa ga mãsu shũkar' dõmin (Allah) Ya fusãtar da kãfirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gãfara da ijãra mai girma.

🎧 Saurara
📜

Fassara — Tafsir

Ma’anonin Kalmomin da ke Bukatar Bayani:

  • شَطْأَهُ: Ƙananan harbe-harben shukar da ke fitowa daga kusa da tushenta.
  • فَآزَرَهُ: Ya taimake shi ya ƙarfafa shi.
  • فَاسْتَغْلَظَ: Ya yi kauri.
  • سُوقِهِ: Tushensa da gangar jikinsa.
  • سِيمَاهُمْ: Alamarsu da kamanninsu.
  • رُكَّعًا سُجَّدًا: Masu ruku’u da sujada a cikin sallarsu.

Fassarar Ayar:

Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallama) Manzon Allah ne, kuma waɗanda suke tare da shi a kan addininsa, masu tsanani ne a kan kafirai, ba su tausayi a gare su ba, amma suna tausayin juna ne a tsakaninsu. Kana ganinsu suna ruku’u da sujada ga Allah a cikin sallarsu, suna neman falala daga Allah da yardarsa. Alamar ibadarsu tana bayyana a fuskokinsu daga tasirin sujada, kamar haske da kyawun hali da natsuwa. Wannan siffarsu ce da aka ambata a cikin Attaura. Kuma siffarsu a cikin Injila kamar shuka ce da ta fito da ƙananan harbe-harbenta, sa’an nan ta taimake su su yi girma, har ta yi kauri kuma ta miƙe tsaye a kan gangar jikinta, tana ba da sha’awa ga manoma. Allah Ya yi wannan misalin ne domin Ya ɓata wa kafirai rai da su, domin ganin yawan muminai da ƙarfinsu da kyawun halinsu. Kuma Allah Ya yi alkawari ga waɗanda suka yi imani da Allah da Manzonsa, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai daga cikin sahabbai, da ya gafarta musu zunubansu, kuma ya ba su lada mai girma wato Aljanna.

Fa’idojin da Ake Ciro Daga Ayar:

  1. Ƙaunar sahabbai (Allah Ya yarda da su) wani ɓangare ne na imani, kuma ƙiyayya da su alama ce ta munafunci da kafirci, domin Allah Ya bayyana cewa ya halicce su don ya ɓata wa kafirai rai.
  2. Kyawawan halaye na muminai: tsananin gaske a kan maƙiyan addini, da tausayi da jin ƙai a tsakanin su, wannan shi ne ma’aunin ƙarfin musulmi.
  3. Alamar ibada tana bayyana a fuskar mai sallata da kyawon hali da annuri, saboda haka ya kamata musulmi ya kiyaye sallarsa don ta kyautata halinsa da fuskarsa.
  4. Misalin shuka yana nuna cewa addinin Musulunci yana girma ne da sahabbai da waɗanda suka bi su da kyau, har ya zama ƙarfi mai ban sha’awa, wanda yake ɓata wa kafirai rai.
  5. Alkawarin Allah gaskiya ne ga dukan waɗanda suka yi imani kuma suka yi aikin ƙwarai, cewa za su sami gafara da lada mai girma, wanda hakan ke ƙarfafa muminai su ci gaba da aikin alheri.


📜 Aya 27-29 — Surah Al-Fath

27لَّقَدْ صَدَقَ اللَّهُ رَسُولَهُ الرُّؤْيَا بِالْحَقِّ ۖ لَتَدْخُلُنَّ الْمَسْجِدَ الْحَرَامَ إِن شَاءَ اللَّهُ آمِنِينَ مُحَلِّقِينَ رُءُوسَكُمْ وَمُقَصِّرِينَ لَا تَخَافُونَ ۖ فَعَلِمَ مَا لَمْ تَعْلَمُوا فَجَعَلَ مِن دُونِ ذَٰلِكَ فَتْحًا قَرِيبًا
Lalle ne haƙĩƙa Allah Ya gaskata wa ManzonSa mafarkinsa da gaskiya: Lalle zã ku shiga Masallacin Harami, in Allah Ya so, kunã mãsu natsuwa, mãsu aske kawunanku da mãsu suisuye, bã ku jin tsõro, dõmin (Allah) Ya san abin da ba ku sani ba, sa'an nan Ya sanya wani cin nasara makusanci a bãyan wannan.
28هُوَ الَّذِي أَرْسَلَ رَسُولَهُ بِالْهُدَىٰ وَدِينِ الْحَقِّ لِيُظْهِرَهُ عَلَى الدِّينِ كُلِّهِ ۚ وَكَفَىٰ بِاللَّهِ شَهِيدًا
Shĩ ne wanda Ya aiki ManzonSa da shiriya da addinin gaskiya dõmin Ya rinjãyar da shi a kan addinai dukansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai shaida.
29مُّحَمَّدٌ رَّسُولُ اللَّهِ ۚ وَالَّذِينَ مَعَهُ أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَمَاءُ بَيْنَهُمْ ۖ تَرَاهُمْ رُكَّعًا سُجَّدًا يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِّنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا ۖ سِيمَاهُمْ فِي وُجُوهِهِم مِّنْ أَثَرِ السُّجُودِ ۚ ذَٰلِكَ مَثَلُهُمْ فِي التَّوْرَاةِ ۚ وَمَثَلُهُمْ فِي الْإِنجِيلِ كَزَرْعٍ أَخْرَجَ شَطْأَهُ فَآزَرَهُ فَاسْتَغْلَظَ فَاسْتَوَىٰ عَلَىٰ سُوقِهِ يُعْجِبُ الزُّرَّاعَ لِيَغِيظَ بِهِمُ الْكُفَّارَ ۗ وَعَدَ اللَّهُ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ مِنْهُم مَّغْفِرَةً وَأَجْرًا عَظِيمًا
Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tãre da shi mãsu tsanani ne a kan kãfirai, mãsu rahama ne a tsakãninsu, kanã ganin su sunã mãsu rukũ'i mãsu sujada, sunã nẽman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alãmarsu tanã a cikin fuskõkinsu, daga kufan sujuda. Wannan shĩ ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injĩla ita ce kamar tsiron shũka wanda ya fitar da rẽshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafãfunsa, yanã bãyar da sha'awa ga mãsu shũkar' dõmin (Allah) Ya fusãtar da kãfirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gãfara da ijãra mai girma.
Al-FathJerin Alqur'ani
29Aya
MedinanRevelation
29Aya

Fassara — Al-Fath 29

Surah Al-Fath Aya 29 - Karatu, Saurara, Fassara, Hausa : Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tãre da…

Surah Aya 29/29 — Surah Al-Fath الفتح (Medinan). Karatu Saurara Fassara (Hausa). Saurara: Surah Al-Fath Saurara, Surah Al-Fath Fassara, Surah Al-Fath mp3, Surah Al-Fath pdf. Aya 27–29. Da Hausa: العربية.




Al-Kur'ani


Monday, September 7, 2026

Don't forget us in your sincere prayers