📖 0/604 shafuka an karanta
📄 371
وَٱجۡعَل لِّي لِسَانَ صِدۡقٍ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ  ۝٨٤ وَٱجۡعَلۡنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ  ۝٨٥ وَٱغۡفِرۡ لِأَبِيٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ  ۝٨٦ وَلَا تُخۡزِنِي يَوۡمَ يُبۡعَثُونَ  ۝٨٧ يَوۡمَ لَا يَنفَعُ مَالٌ وَلَا بَنُونَ  ۝٨٨ إِلَّا مَنۡ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلۡبٍ سَلِيمٍ  ۝٨٩ وَأُزۡلِفَتِ ٱلۡجَنَّةُ لِلۡمُتَّقِينَ  ۝٩٠ وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِلۡغَاوِينَ  ۝٩١ وَقِيلَ لَهُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ  ۝٩٢ مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلۡ يَنصُرُونَكُمۡ أَوۡ يَنتَصِرُونَ  ۝٩٣ فَكُبۡكِبُواْ فِيهَا هُمۡ وَٱلۡغَاوُۥنَ  ۝٩٤ وَجُنُودُ إِبۡلِيسَ أَجۡمَعُونَ  ۝٩٥ قَالُواْ وَهُمۡ فِيهَا يَخۡتَصِمُونَ  ۝٩٦ تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَٰلٍ مُّبِينٍ  ۝٩٧ إِذۡ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ  ۝٩٨ وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلۡمُجۡرِمُونَ  ۝٩٩ فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ  ۝١٠٠ وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍ  ۝١٠١ فَلَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ  ۝١٠٢ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةًۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ  ۝١٠٣ وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ  ۝١٠٤ كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ  ۝١٠٥ إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ  ۝١٠٦ إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٌ  ۝١٠٧ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ  ۝١٠٨ وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ  ۝١٠٩ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ  ۝١١٠ ۞ قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ  ۝١١١
26:84
وَٱجۡعَل لِّي لِسَانَ صِدۡقٍ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ  ۝٨٤
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."
26:85
وَٱجۡعَلۡنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ  ۝٨٥
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
26:86
وَٱغۡفِرۡ لِأَبِيٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ  ۝٨٦
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
26:87
وَلَا تُخۡزِنِي يَوۡمَ يُبۡعَثُونَ  ۝٨٧
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
26:88
يَوۡمَ لَا يَنفَعُ مَالٌ وَلَا بَنُونَ  ۝٨٨
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
26:89
إِلَّا مَنۡ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلۡبٍ سَلِيمٍ  ۝٨٩
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
26:90
وَأُزۡلِفَتِ ٱلۡجَنَّةُ لِلۡمُتَّقِينَ  ۝٩٠
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
26:91
وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِلۡغَاوِينَ  ۝٩١
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
26:92
وَقِيلَ لَهُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ  ۝٩٢
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
26:93
مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلۡ يَنصُرُونَكُمۡ أَوۡ يَنتَصِرُونَ  ۝٩٣
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
26:94
فَكُبۡكِبُواْ فِيهَا هُمۡ وَٱلۡغَاوُۥنَ  ۝٩٤
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.
26:95
وَجُنُودُ إِبۡلِيسَ أَجۡمَعُونَ  ۝٩٥
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
26:96
قَالُواْ وَهُمۡ فِيهَا يَخۡتَصِمُونَ  ۝٩٦
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
26:97
تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَٰلٍ مُّبِينٍ  ۝٩٧
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
26:98
إِذۡ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ  ۝٩٨
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
26:99
وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلۡمُجۡرِمُونَ  ۝٩٩
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
26:100
فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ  ۝١٠٠
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
26:101
وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍ  ۝١٠١
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
26:102
فَلَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ  ۝١٠٢
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
26:103
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةًۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ  ۝١٠٣
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
26:104
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ  ۝١٠٤
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
26:105
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ  ۝١٠٥
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
26:106
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ  ۝١٠٦
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
26:107
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٌ  ۝١٠٧
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
26:108
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ  ۝١٠٨
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
26:109
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ  ۝١٠٩
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
26:110
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ  ۝١١٠
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
26:111
۞ قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ  ۝١١١
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"


📚Juz 19 📄371 / 604



Mishary Rashid Alafasy
Mahmoud Khalil Al-Husary
Abdurrahman As-Sudais
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
Abdul Basit Abdul Samad
Ali Al-Hudhaify
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
Abu Bakr Ash-Shaatree
Muhammad Ayyoub
Abdullah Basfar
Abdullah Al-Juhani
Maher Al Muaiqly
0:00
0:00
-

Al-Kur'ani


Wednesday, August 26, 2026

Don't forget us in your sincere prayers