Surah Al-Mu'minun
PDF —
118 Aya Meccan PDF
Built right in your browser — download starts automatically

Surah Al-Mu'minun pdf — Sauke (Hausa)

Surah Al-Mu'minun pdf Hausa — Sauke Surah Al-Mu'minun Fassara. Al-Mu'minun (Meccan) 118 Aya.



Surah Al-Mu'minun
118 Aya · Meccan · Hausa
bismillah
ﭑﭒﭓﭔ
Lalle ne, Mũminai sun sãmi babban rabõ.
ﭕﭖﭗﭘﭙﭚ
Waɗanda suke a cikin sallarsu mãsu tawãli'u ne.
ﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
Kuma waɗanda suke, sũdaga barin yasassar magana, mãsu kau da kai ne.
ﭡﭢﭣﭤﭥ
Kuma waɗanda suke ga zakka mãsu aikatãwa ne.
ﭦﭧﭨﭩﭪ
Kuma waɗanda suke ga farjõjinsu mãsu tsarẽwa ne.
ﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵ
Fãce a kan mãtan aurensu, kõ kuwa abin da hannayen dãmansu suka mallaka to lalle sũ bã waɗanda ake zargi, ba, ne.
ﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽ
Sabõda haka wanda ya nẽmi abin da ke bãyan wancan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙẽtarẽwar haddi.
ﭾﭿﮀﮁﮂﮃ
Kuma waɗanda suke, sũga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
ﮄﮅﮆﮇﮈﮉ
Kuma da waɗanda suke, sũ a kan sallõlinsu sunã tsarẽwa.
ﮊﮋﮌﮍ
Waɗannan, sũ ne magãda.
ﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
Waɗanda suke gãdõn (Aljannar) Firdausi, su a cikinta madawwama ne.
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga lãka.
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
Sa'an nan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya.
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
Sa'an nan kuma Muka halitta shi gudan jini, sa'an nan Muka halitta gudan jinin tsõka, sa'an nan Muka halitta tsõkar ta zama ƙasũsuwa, sa'an nan Muka tufãtar da ƙasũsuwan da wani nãma sa'an nan kuma Muka ƙãga shi wata halitta dabam. Sabõda haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyaun mãsu halittawa.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
Sa'an nan kuma ku, bãyan wannan, lalle ne masu mutuwa ne.
ﯢﯣﯤﯥﯦﯧ
Sa'an nan kuma lalle ne kũ a Rãnar ¡iyãma, za a iãyar da ku,
ﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲ
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun halitta, a samanku, hanyõyi bakwai, kuma ba Mu kasance, daga barin halittar, Mãsu shagala ba.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟ
Muka saukar da ruwa daga sama bisa gwargwado, sa'an nan Muka zaunar da shi a cikin ƙasa alhãli, lalle ne Mũ, a kan tafiyar da shi, Mãsu iyãwa ne.
ﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭ
Sai Muka ƙãga muku, game da shi (ruwan), gõnaki daga daĩnai da inabõbi, kunã da, a cikinsu, 'ya'yan itãcen marmari mãsu yawa, kuma daga gare su kuke ci.
ﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷ
Da wata itãciya, tanã fita daga dũtsin Sainã'a, tanã tsira da man shãfãwa, da man miya dõmin masu cĩ.
ﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
Kuma lalle ne kunã da abin lũra a cikin dabbõbin ni'imõmi Munã shãyar da ku daga abin da yake a cikinsu, kuma kunã da a cikinsu abũbuwan amfãni mãsu yawa, kuma daga gare su kuke cĩ
ﮉﮊﮋﮌﮍ
Kuma a kansu da a kan jirgin ruwa ake ɗaukar ku.
ﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnensa, sai ya ce: "Yã mutãnẽna! Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa waninsa. Shin, to, bã za ku yi taƙawa ba?"
ﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
Sai mashãwarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa, suka ce: "Wannan ba kõwa ba ne, fãce mutum misãlinku, yanã nufin ya ɗaukaka a kanku. Dã Allah Yã so, lalle ne dã Yã saukar da Malã'iku, Ba muji (kõme) ba, game da wannan, a cikin ubanninmu na farko."
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
"Shi bai zamo kõwa ba fãce wani namiji ne, a gare shi akwai hauka, sai ku yi jinkiri da shi har wani lõkaci."
ﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka taimakeni sabõda sun ƙaryatani."
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎ
Sai Muka yi wahayi zuwa gare shi. "Ka sana'anta jirgin bisa ga idonMu, da wahayinMu. To, idan umuminMu ya jẽ, kuma tandã ta ɓuɓɓuga da ruwa, to, ka shigar a cikinta daga kõme, ma'aura biyu, da iyãlanka, sai wanda Magana ta gabãta a kansa, daga gare su, kuma kada ka rõƙẽ Ni (sabõda wani) a cikin waɗanda suka yi zãlunci, lalle ne sũ waɗanda ake nutsarwa ne.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
"Sa'an nan idan ka daidaitu kai da waɗanda ke tãre da kai a kan jirgin, sai ka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya tsĩrar damu daga mutãne azzãlumai."
ﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩ
"Kuma ka ce: 'Ya Ubangijĩna! Ka saukar da ni, saukarwa mai albarka. Kuma Kai ne Mafi alhẽrin mãsu saukarwa.'"
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱ
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi, ko da yake Mun kasance, haƙẽƙa' Mãsu jarrabãwa.
ﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
Sa'an nan kuma Muka ƙãga wani ƙarni na waɗansu dabam daga bãyansu.
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
Sai Muka aika a cikinsu Manzo daga gare su. "Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa, sai Shi. Shin to, bã zã ku yi taƙawa ba?"
ﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
Mashãwarta daga mutãnensa, waɗanda suka kãfirta kuma suka ƙaryata game da haɗuwa da Lãhira, kuma Muka ni'imtar da su a cikin rãyuwar dũniya, suka ce: "Wannan bã kõwa ba fãce wani mutum ne kamarku, yanã cĩ daga abin da kuke cĩ daga gare shi, kuma yanã shã daga abin da kuke shã."
ﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
"Kuma lalle ne idan kun yi ɗã' a ga mutum misãlinku, lalle ne, a lõkacin nan, haƙĩƙa, kũ mãsu hasãra ne."
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕ
"Shin, yanã yi muku wa'adin (cẽwa) lalle kũ, idan kun mutu kuma kuka kasance turɓãya da ɓasũsuwa lalle ne kũ waɗanda ake fitarwa ne?"
ﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
"Faufau faufau ga abin da ake yi muku wa'adi da shi."
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
"Rãyuwa ba ta zama ba fãce rãyuwarmu ta dũniya, munã mutuwa kuma munã rãyuwa, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
ﯧﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳ
"Bai zama kõwa ba fãce namiji, ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma ba mu zama, sabõda shi, mãsu ĩmãni ba."
ﯴﯵﯶﯷﯸﯹ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka taimake ni sabõda sun ƙaryatã ni."
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿ
Ya ce: "Daga abu kaɗan, lalle ne zã su wãyi gari sunã mãsu nadãma."
ﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
Sai tsãwa ta kãma su da gaskiya, sai Muka sanya su tunkuɓa. Sabõda haka nĩsa ya tabbataga mutãne azzãlumai!
ﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐ
Sa'an kuma Muka ƙãga halittar wasu ƙarnõni dabam daga bayãnsu.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘ
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
ﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
Sa'an nan kuma Muka aika da ManzanninMu jẽre a kõda yaushe Manzon wata al'umma ya jẽ mata, sai su ƙaryata shi, sabõda haka Muka biyar da sãshensu ga sãshe, kuma Muka sanya su lãbãrun hĩra. To, nĩsa ya tabbata ga mutãne (waɗanda) bã su yin ĩmãni!
ﭰﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
Sa'an nan kuma Muka aika Mũsã da ɗan'uwansa Hãrũna, game da ãyõyinMu da, dalĩli bayyananne.
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
Zuwa ga Fir'auna da majalisarsa, sai suka kangara, alhãli sun kasance mutãne ne marinjãya.
ﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
Sai suka ce: "Shin, zã Mu yi ĩmãni sabõda wasu mutãne biyu misãlinmu, alhãli kuwa mutãnensu a gare mu, mãsu bauta ne."
ﮉﮊﮋﮌﮍ
Sai suka ƙaryata su sabõda haka suka kasance halakakku.
ﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã littãfi tsammaninsu zã su shiryu.
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
Kuma Mun sanya ¦an Maryama, shi da uwarsa wata ãyã Kuma Muka tattara su zuwa ga wani tsauni ma'abũcin natsuwa da marẽmari.
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
Yã ku Manzanni! Ku ci daga abũbuwa mãsu dãɗi kuma ku aikata aikin ƙwarai. Lalle Nĩga abin da kuke aikatãwa, Masani ne.
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗ
Kuma lalle ne, wannan al'ummarku ce, al'umma guda, kuma Nĩ, Ubangijinku ne, sai ku bĩ Ni da taƙawa.
ﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
Sai (al'ummar) suka yanyanke al'amarinsu a tsakãninsu guntu-guntu, kõwace ƙungiya sunã mãsu farin ciki da abin da yake a gare su.
ﯣﯤﯥﯦﯧﯨ
To, ka bar su a cikin ɓatarsu har a wani lõkaci.
ﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰ
Shin, sunã zaton cẽwa abin da Muke taimakon su da shi daga dũkiya da ɗiya,
ﯱﯲﯳﯴﯵﯶﯷﯸﯹ
Munã yi musu gaggãwa ne a cikin alhẽrõri?
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁ
Lalle ne waɗanda suke mãsu sauna sabo da tsõron Ubangijinsu,
ﰂﰃﰄﰅﰆﰇ
Da waɗanda suke, game da ãyõyin Ubangijinsu sunã ĩmãni,
ﰈﰉﰊﰋﰌﰍ
Da waɗanda suke game da Ubangijinsu bã su yin shirki,
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛ
Da waɗanda ke bãyar da abin da suka bãyar, alhãli kuwa zukãtansu sunã tsõrace dõmin sunã kõmãwa zuwa ga Ubangijinsu,
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
Waɗancan sunã gaggãwar tsẽre a cikin ayyukan alhẽri, alhãli kuwa sunã mãsu tsẽrẽwa zuwa gare su (ayyukan alhẽri).
ﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱ
Kuma bã Mu kallafa wa rai fãce abin iyawarsa, kuma a wurinMu akwai wani Littãfi wanda yake magana da gakiya, kuma sũ bã a zãluntar su.
ﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
Ã'a, zukãtansu sunã cikin jãhilci daga wannan (magana), kuma sunã da waɗansu ayyuka, baicin wancan, sũ a gare su, mãsu aikatãwa ne.
ﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉ
Har idan Mun kãma mani'imtansu da azãba, sai gã su sunã hargõwa.
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒ
Kada ku yi hargowa a yau, lalle ne kũ, daga gare Mu bã a taimakon ku.
ﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
Lalle ne, ãyõyĩNa sun kasance anã karãtun su a kanku, sai kuka kasance, a kan dugãduganku, kunã kõmãwa bãya.
ﮝﮞﮟﮠﮡ
Kunã mãsu girman kai gare shi (Annabi), da hĩrã kunã alfãsha.
ﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
Shin fa, ba su yi ta'ammalin maganar (Alƙur'ãni) ba, kõ abin da bai jẽ wa ubanninsu na farko ba ne ya jẽ musu?
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕ
Kõ ba su san Manzonsu ba ne dõmin haka suke mãsu musu a gare shi?
ﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
Kõ sunã cẽwa, "Akwai hauka gare shi?" Ã'a, yã zo musu da gaskiya, alhãli kuwa mafi yawansu, ga gaskiya, mãsu ƙi ne.
ﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳ
Kuma dã gaskiya (Alƙur'ãni) yã bi son zuciyoyinsu, haƙĩƙa dã sammai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sun ɓãci. Ã'a, Mun tafo musu da ambaton (darajar) su, sa'an nan sũ daga barin ambaton su mãsu bijirẽwa ne, bijirẽwa.
ﯴﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾ
Kõ kanã tambayar su wani harãji ne (a kan iyar da Manzanci a gare su)? To, harãjin Ubangijinka ne mafi alhẽri kuma Shĩ ne Mafi alhẽrin mãsu ciyarwa.
ﯿﰀﰁﰂﰃﰄ
Kuma lalle ne kai haƙĩƙa kanã kiran su zuwa ga hanya madaidaiciya.
ﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍ
Kuma lalle waɗanda ba su yi ĩmãni da Lãhira ba mãsu karkacẽwa daga hanya ne.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
Kuma dã Mun ji tausayinsu, kuma Muka kuranye musu abin da yake tãre da su na cũta, lalle ne dã sun yi zurfi a cikin ɓatarsu, sunã ɗimuwa.
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã kãma su da azãba sai dai ba su saukar da kai ba, ga Ubangijinsu, kama bã su yin tawãli'u.
ﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
Har idan Mun bũɗe, akansu, wata ƙõfa mai azãba mai tsanani sai gã su a cikinta sunã mãsu mugi.
ﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
Kuma Shi ne Wanda Ya ƙãga halittar ji da gani da zukãta dominku. Kaɗan ƙwarai kuke gõdẽwa.
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
Kuma Shĩ ne Ya halitta ku a cikin ƙasa, kuma zuwa gare Shi ake tãyar da ku.
ﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓ
Kuma Shĩ ne Wanda Yake rãyarwa, kuma Yanã matarwa, kuma a gare Shi ne sãɓawar dare da yini take. Shin, to, bã zã ku hankalta ba?
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
Ã'a, sun faɗi misãlin abin da na farko suka faɗa.
ﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
Suka ce: "Shin idan mun mutu kuma muka kasance turɓaya da ƙasũsuwa shin lal1e ne mu haƙĩƙa waɗanda ake tãyarwa ne?
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰ
"Lalle ne, haƙĩƙa, an yi mana wa'adi, mũ da ubanninmu ga wannan a gabãni, wannan abu bai zama kõme ba, fãce tãtsũniyõyin na farko."
ﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚ
Ka ce: "Wane ne da mulkin ƙasa da wanda ke a cikinta, idan kun kasance kunã sani?"
ﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
Zã su ce: "Ta Allah ne." Ka ce, "Shin, to, bã zã ku yi tunãni ba?"
ﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪ
Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai bakwai kuma Ubangijin Al'arshi mai girma?"
ﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱ
Zã su ce: "Na Allah ne." Ka ce, "Shin, to, bã zã ku bĩ Shi da taƙawa ba?"
ﯲﯳﯴﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀ
Ka ce: "Wãne ne ga hannunsa mallakar kõwane abu take alhãli kuwa shi yanã tsarẽwar wani, kuma ba a tsare kõwa daga gare shi, idan kun kasance kunã sani?"
ﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇ
Zã su ce: "Ga Allah yake." Ka ce: "To, yãya ake sihirce ku?"
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
Ã'a, Mun zo musu da gaskiya, kuma lalle ne sũ, haƙĩƙa, maƙaryata ne.
ﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱ
Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwane abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa.
ﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
Masanin ɓõye da bayyane. sa'an nan Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka.
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
Ka ce: "Yã Ubangijina! Ko dai Ka nũna mini abin da ake yi musu wa'adi da shi."
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆ
"Yã Ubangijina, to, kada Ka sanya ni a cikin mutãne azzãlumai."
ﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
Kuma lalle ne Mũ haƙĩƙa Mãsu iyawa ne a kan Mu nũna maka abin da Muke yi musu wa'adi da shi.
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
Ka tunkuɗe cũta da wadda take ita ce mafi kyau. Mũ neMafi sani game da abin da suke siffantãwa.
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡ
Ka ce: "Yã Ubangijĩna, inã nẽman tsari da Kai daga fizge-fizgen Shaiɗãnu."
ﮢﮣﮤﮥﮦﮧ
"Kuma inã nẽman tsari da Kai, ya Ubangijĩna! Dõmin kada su halarto ni, "
ﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰ
Har idan mutuwa ta jẽ wa ɗayansu, sai ya ce: "Yã Ubangijina, Ku mayar da ni (dũniya)."
ﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥ
"Tsammãnina in aikata aiki na ƙwarai cikin abin da na bari." Kayya! Lalle ne ita kalma ce, shĩ ne mafaɗinta, alhãli kuwa a bãya gare su akwai wani shãmaki har rãnar da zã a tãyar da su.
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰ
Sa'an nan idan an yi bũsa a cikin ƙaho, to, bãbu dangantakõki a tsakãninsu a rãnar nan kuma bã zã su tambayi jũnansu ba.
ﯱﯲﯳﯴﯵﯶﯷ
To, wadanda sikẽlinsu ya yi nauyi, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
ﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂ
Kuma waɗanda sikẽlinsu ya yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasãrar rãyukansu sunã madawwama a cikin Jahannama.
ﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
Fuskokinsu sunã balbalar wuta, kuma su a cikinta mãsu yãgaggun leɓɓa daga haƙõra ne.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙ
"Shin, ayõyĩNa ba su kasance anã karanta su a kanku ba sai kuka kasance game da su kunã ƙaryatãwa?"
ﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢ
Suka ce: "Yã Ubangijinmu, shaƙãwamiu ce ta rinjãya a kanmu, kuma mun kasance mutãne ɓatattu."
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪ
"Yã Ubangjinmu! Ka fitar da mu daga gare ta, sa'an nan idan mun kõma, to, lalle ne, mũ ne mãsu zãlunci."
ﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
Ya ce: "Ku tafi (da wulãkanci) a cikinta. Kada ku yi Mini magana."
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
Lalle ne waɗansu ƙungiyoyi daga bãyiNa sun kasance sunã cẽwa, "Yã Ubangijinmu! Mun yi ĩmãni, sai Ka gãfarta mana, kuma Ka yi mana rahama, kuma Kai ne Mafi alhẽrin mãsu tausayi."
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
Sai kuka riƙe su lẽburõri har suka mantar da ku ambatõNa kuma kun kasance, daga gare su kuke yin dãriya.
ﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
Lalle ne Nĩ Inã sãka musu a yau, sabõda abin da suka yi wa haƙuri. Dõmin lalle ne sũ sũ ne mãsu sãmun babban rabo.
ﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
Ya ce: "Nawa kuka zauna a cikin ƙasa na ƙidãyar shẽkaru?"
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
Suka ce: "Mun zauna a yini ɗaya ko rabin yini, sai ka tambayi mãsu ƙidãyãwa."
ﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
Ya ce: "Ba ku zauna ba fãce kaɗan, dã dai kun kasance kunã sani."
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗ
"Shin, to, kun yi zaton cẽwa Mun halitta ku ne da wãsa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, bã zã ku kõmo ba?"
ﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤ
Allah Mamallaki gaskiya, Yã ɗaukaka. Bãbu abin bautãwa, fãce Shi. Shĩ ne Ubangijin Al'arshi, mai daraja.
ﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶﯷﯸ
Kuma wanda ya kira, tãre da Allah, waɗansu abũbuwan bautãwa na dabam, bã yanã da wani dalĩli game da shĩ (kiran) ba, to hisãbinsa yanã wurin Ubangijinsa kawai. Lalle ne, kãfirai bã su cin nasara.
ﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀ
Kuma ka ce: "Yã Ubangijina! Ka yi gãfara, Ka yi rahama, kuma Kai ne Mafi alhẽrin mãsu rahama."

Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers