سورة النازعات بالهوسا

  1. استمع للسورة
  2. سور أخرى
  3. ترجمة السورة
القرآن الكريم | ترجمة معاني القرآن | اللغة الهوسا | سورة النازعات | Naziat - عدد آياتها 46 - رقم السورة في المصحف: 79 - معنى السورة بالإنجليزية: Those Who Tear Out.

وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا(1)

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا(2)

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا(3)

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا(4)

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا(5)

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ(6)

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ(7)

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ(8)

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ(9)

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ(10)

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةً(11)

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ(12)

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ(13)

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِ(14)

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ(15)

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى(16)

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ(17)

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰ أَن تَزَكَّىٰ(18)

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ(19)

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ(20)

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ(21)

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ(22)

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ(23)

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ(24)

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ(25)

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰ(26)

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا(27)

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا(28)

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا(29)

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا(30)

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا(31)

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا(32)

Da duwatsu, Yã kafe ta.

مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ(33)

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ(34)

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ مَا سَعَىٰ(35)

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ(36)

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ(37)

To, amma wanda ya yi girman kai.

وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا(38)

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ(39)

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ(40)

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ(41)

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا(42)

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَا(43)

Me ya haɗã ka da ambatonta?

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَاهَا(44)

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَا(45)

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا(46)

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.


المزيد من السور باللغة الهوسا:

سورة البقرة آل عمران سورة النساء
سورة المائدة سورة يوسف سورة ابراهيم
سورة الحجر سورة الكهف سورة مريم
سورة السجدة سورة يس سورة الدخان
سورة النجم سورة الرحمن سورة الواقعة
سورة الحشر سورة الملك سورة الحاقة

تحميل سورة النازعات بصوت أشهر القراء :

قم باختيار القارئ للاستماع و تحميل سورة النازعات كاملة بجودة عالية
سورة النازعات أحمد العجمي
أحمد العجمي
سورة النازعات خالد الجليل
خالد الجليل
سورة النازعات سعد الغامدي
سعد الغامدي
سورة النازعات سعود الشريم
سعود الشريم
سورة النازعات عبد الباسط عبد الصمد
عبد الباسط
سورة النازعات عبد الله عواد الجهني
عبد الله الجهني
سورة النازعات علي الحذيفي
علي الحذيفي
سورة النازعات فارس عباد
فارس عباد
سورة النازعات ماهر المعيقلي
ماهر المعيقلي
سورة النازعات محمد جبريل
محمد جبريل
سورة النازعات محمد صديق المنشاوي
المنشاوي
سورة النازعات الحصري
الحصري
سورة النازعات العفاسي
مشاري العفاسي
سورة النازعات ناصر القطامي
ناصر القطامي
سورة النازعات ياسر الدوسري
ياسر الدوسري



Monday, April 29, 2024

لا تنسنا من دعوة صالحة بظهر الغيب