Surah Sad
88 Aya · Meccan · Hausa
bismillah
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
Ṣ̃, Inã rantsuwa da Al-ƙur'ãni mai hukunce-hukunce.
ﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
Ã'a, waɗanda suka kãfirta sunã cikin girman kai (ga rikon al'ãdunsu) da sãɓãni (tsakãnin jũnansu).
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
Da yawa Muka halakar da wani ƙarni, a gabãninsu, suka yi kira (nẽman cẽto), bãbu lõkacin kuɓucewa.
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
Kuma suka yi mãmãki dõmin Mai gargaɗi, daga cikinsu, ya je musu. Kuma kãfirai sukace, "Wannan mai sihiri ne, maƙaryaci."
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
"Shin, yã sanya gumãka duka su zama abin bautawa guda? Lalle wannan, haƙĩƙa, abu ne mai ban mãmaki!"
ﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌ
Shũgabanni daga cikinsu, suka tafi (suka ce),"Ku yi tafiyarku, ku yi haƙuri a kan abũbuwan bautawarku. Lalle wannan, haƙiƙa, wani abu ne ake nufi!"
ﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗ
"Ba mu taɓa ji ba, game da wannan a cikin addinin ƙarshe. Wannan bai zama ba fãce ƙiren ƙarya."
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
"Shin, an saukar da Alƙur'ãni ne a kansa, a tsakãninmu (mũ kuma ba mu gani ba)?" Ã'a, su dai sunã cikin shakka daga hukunciNa Ã'a, ba su i da ɗanɗanar azãba ba.
ﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱ
Ko kuma a wurinsu ne ake ajiye taskõkin rahamar Ubangijinka, Mabuwãyi, Mai yawan kyauta?
ﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞ
Kõ kuma sũ ne da mallakar sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu? To sai su hau a cikin sammai (dõmin, su hana saukar Alƙur'ãni ga Muhammadu).
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥ
Rundunõni ne abin da ke can, rusassu, na ƙungiyõyinsu.
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, da Ãdãwa da Fir'auna mai turãkun (da suka kafe mulkinsa).
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶﯷ
Da Samũdãwa da mutãnen Luɗu da ma'abũta ƙunci, waɗancan ne ƙungiyõyin.
ﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿ
Bãbu kõwa a cikinsu fãce ya ƙaryata Manzanni, sabõda haka azãbãTa ta wajaba.
ﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊ
Kuma waɗannan bã su jiran kõme fãce tsãwã guda, wadda bã ta da hani.
ﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑﰒﰓ
Kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka gaggauta mana da rabonmu, a gabãnin rãnar bincike."
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
Ka yi haƙuri bisa ga abin da suke faɗa (na izgili), kuma ka ambaci bãwanMu Dãwũda ma'abũcin ƙarfin ibãda. Lalle, shi, mai mayar da al'amari ga Allah ne.
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥ
Lalle Mũ, Mun hõre duwãtsu tãre da shi, sunã yin tasbĩhi maraice da fitõwar rãnã.
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
Da tsuntsãye waɗanda ake tattarawa, kõwannensu mai kõmãwa ne a gare shi.
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
Kuma Muka ƙarfafa mulkinsa, kuma Muka bã shi hikima da rarrabẽwar magana.
ﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼ
Kuma shin, lãbãrin mãsu husũma ya zo maka, a lõkacin da suka haura gãrun masallaci?
ﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
A lõkacin da suka shiga ga Dãwũda, sai ya firgita daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro, masu husuma biyu ne; sãshenmu ya zãlunci sãshe. Sabõda haka, ka yi hakunci a tsakãninmu da gaskiya. Kada ka ƙẽtare haddi kuma ka shiryar da mu zuwa, ga tsakar hanya."
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
"Lalle wannan dan'uwãna ne, yanã da tunkiya casa'in da tara, kuma inã da tunkiya guda, sai ya ce: 'Ka lãmunce mini ita. Kuma ya buwãye ni ga magana."
ﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫ
(Dãwũda) ya ce: "Lalle, haƙiƙa ya zãlunce ka game da tambayar tunkiyarka zuwa ga tumakinsa. Kuma lalle ne mãsu yawa daga abõkan tarayya, haƙiƙa, sãshensu na zambatar sãshe fãce waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai." Kuma Dãwũda ya tabbata cẽwa Mun fitine shi ne, sabõda haka, ya nẽmi Ubangijinsa gãfara, kuma ya fãɗi yanã mai sujada, kuma ya mayar da al'amari ga Allah.
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶ
Sabõda haka Muka gãfarta masa wancan, kuma lalle yanã da wata kusantar daraja a wurinMu, da kyaun makõma.
ﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕﰖ
Yã Dãwũda! Lalle Mũ Mun sanya ka Halĩfa a cikin ƙasã. To, ka yi hukunci tsakãnin mutãne da gaskiya, kuma kada ka biye wa son zũciyar, har ya ɓatar dakai daga hanyar Allah. Lalle waɗanda ke ɓacẽwa daga hanyar Allah sunã da wata azãba mai tsanani dõmin abin da suka manta, a rãnar hisãbi
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
Kuma ba Mu halitta sama da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu ba a kan ƙarya. Wannan shĩ ne zaton waɗanda suka kãfirta. To, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta daga wutã.
ﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱ
Kõ zã Mu sanya waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai kamar waɗanda suke mãsu barna ne a cikin ƙasa? Ko kuma za Mu sanya masu bin Allah da taƙawa kamar fãjirai makarkata?
ﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻ
(Wannan) Littãfi ne, Mun saukar da shi zuwa gare ka, yanã, mai albarka, dõmin su lũra da ãyõyinsa, kuma don mãsu hankali su riƙa yin tunãni.
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄ
Kuma Muka bai wa Dãwũda Sulaimãn. Mãdalla da bãwanMu, shi. Lalle shi (Sulaimãn) mai mayar da al'amari ne ga Allah.
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋ
A lõkacin da aka gitta masa dawãki mãsu asali, a lõkacin maraice.
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗ
Sai ya ce: "Lalle nĩ, na fĩfĩta son dũkiya daga tunãwar Ubangijina, har (rãnã) ta faku da shãmaki!"
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
"Ku mayar da su a gare ni." Sai ya shiga yankansu da takõbi ga ƙwabrukansu da wuyõyinsu.
ﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
Kuma lalle haƙĩƙa, Mun fitini Sulaiman kuma Muka jẽfa wani jikin mutum a kan karagarsa. Sa'an nan ya mayar da al'amari zuwa gare Mu.
ﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka gãfarta mini, kuma Ka bã ni mulki wanda bã ya kamãta da kõwa daga bãyãna. Lalle Kai, Kai ne Mai yawan kyauta.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤ
Sabõda haka Muka hõre masa iska tanã gudu da umurninsa, tãna tãshi da sauƙi, inda ya nufa.
ﯥﯦﯧﯨﯩ
Da shaiɗanu dukan mai gini, da mai nutsa (a cikin kõguna.)
ﯪﯫﯬﯭﯮ
Waɗansu, ɗaɗɗaure a cikin marũruwa.
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶ
Wannan kyautarMu ce. Sai ka yi kyauta ga wanda kake so, ko kuma ka riƙe, bãbu wani bincike.
ﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
Kuma lalle, haƙĩƙa yanã da kusantar daraja a wurinMu da kyaun makõma.
ﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
Kuma ka ambaci bãwanMu Ayyũba a lõkacin da ya kirãyi Ubangijinsa, ya ce: "Lalle nĩ, Shaiɗan yã shãfe ni da wahala da kuma wata azãba."
ﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑ
Ka shura da ƙafarka. Wannan abin wanka ne mai sanyi da abin shã.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛ
Kuma Muka bã shi iyalansa da kwatankwacinsu tãre da su sabõda rahama daga gare Mu, da tunãtarwa ga mãsu hankali.
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
Kuma ka riƙi wata ƙulla da hannunka, ka yi dũka da ita kuma kada ka karya rantsuwarka. Lalle Mũ, Mun sãme shi mai haƙuri. Madalla da bãwa, shĩ Lalle shĩ mai mayar da al'amari ga Allah ne.
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵ
Kuma ka ambaci bãyinMu: Ibrahĩm da ls'hãƙa da Ya'aƙũba, ma'abũta ƙarfin (ɗaukar umurninMu) da basĩra.
ﭶﭷﭸﭹﭺﭻ
Lalle Mũ, Mun keɓance su game da wata, tsattsarkar aba: Hukunce-hukuncen gidan dũniya (mai tunãtar da su Lãhira).
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
Kuma lalle sũ a wurinMu, tabbas, sunã daga zãɓaɓɓu, mafĩfĩta.
ﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋ
Kuma ka ambaci Isma'ĩla da llyãs da Zulkifli, kuma dukansu sunã daga zãɓaɓɓu.
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓ
Wannan tunãtarwa ce, kuma lalle mãsu bin Allah da taƙawa, sunã da kyakkyawar makõma.
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
Gidãjen Aljannar zama, alhãli kuwa tanã abar buɗe wa kõfõfi sabõda su.
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡ
Sunã gingincire a cikinsu, sunã kira a cikinsu, ga 'ya'yan itãcen marmari mãsu yawa, da abin shã.
ﮢﮣﮤﮥﮦﮧ
Kuma a wurinsu akwai mãtan aure mãsu gajarta ganinsu ga mazansu, tsãrar jũna.
ﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
Wannan shĩ ne abin da ake yi muku wa'adi ga rãnar hisãbi.
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
Lalle wannan, haƙĩƙa, azurtarwarMu ce, bã ta ƙãrẽwa.
ﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝ
Wannan shĩ ne kuma lalle makangara, haƙĩƙa, sunã da mafi sharrin makõma.
ﯞﯟﯠﯡﯢ
Jahannama, sunã shigarta. To, shimfiɗar tã mũnana, ita.
ﯣﯤﯥﯦﯧ
Wannan shĩ ne! To, su ɗanɗane shi: ruwan zãfi ne da ruɓaɓɓen jini.
ﯨﯩﯪﯫﯬ
Da wani daga siffarsa nau'i-nau'i.
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶﯷﯸ
Wannan wani yanki ne mai kũtsawa tãre da ku, bãbu marãba a gare su, lalle sũ, mãsu shiga Wutã ne.
ﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆ
Suka ce: "Ã'a, ku ne bãbu marãba a gare ku, kũ ne kuka gabãtar da shi a gare mu." To, matabbatar tã mũnana (ita wutar).
ﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑﰒ
Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Wanda ya gabãtar da wannan a gare mu, to, Ka ƙãra masa azãba, ninki, a cikin wutã."
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛ
Kuma suka ce: "Mẽ ya sãme mu, bã mu ganin waɗansu mazãje, mun kasance munã ƙidãya su daga asharãrai?"
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢ
"Shin, mun riƙe su abin izgili ne kõ idãnunmu sun karkata daga gare su ne?"
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩ
Lalle wannan, haƙĩƙa, gaskiya ne, husũmar mutãnen wutã.
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵﭶ
Ka ce: "Nĩ mai gargaɗikawai ne, kuma babu wani abin bautawa sai Allah, Makaɗaici, Mai tilastawa."
ﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
"Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu Mabuwãyi, Mai gãfara."
ﭿﮀﮁﮂﮃ
Ka ce: "Shĩ (Alkur'ãni) babban lãbãri ne mai girma".
ﮄﮅﮆﮇ
"Kũ, mãsu bijirẽwa ne daga gare shi!"
ﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
"Wani ilmi bai kasance a gare ni ba game da jama'a (malã'iku) mafi ɗaukaka a lõkacin da suke yin husũma."
ﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
"Ba a yi mini wahayin kõme ba face cẽwa ni mai gargaɗi kawai ne, mai bayyanãwa."
ﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤ
A lõkacin da Ubangijinka Ya ce wa malã'iku, "Lalle Nĩ Mai halitta mutum ne daga lãkã.
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮ
"Sa'an nan idan Nã daidaita shi, kuma Na hũra (wani abu) daga RuhĩNa a cikinsa to ku fãɗi kunã mãsu sujada a gare; shi."
ﮯﮰﮱﯓﯔ
Sai malã'ikun suka yi sujada dukansu, gabã ɗaya.
ﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
Fãce Iblis, ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫ
(Allah) Ya ce, "Yã Ibilis! Mẽ ya hana ka, ka yi sujada ga abin da Nã halitta da HannayeNa biyu? Shin, kã yi girman kai ne, kõ kuwa kã kasance daga maɗaukaka ne?"
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶ
Ya ce, "Nĩ, mafifici ne daga gare shi: Kã halitta ni daga wutã, kuma Kã halitta shi daga lãkã."
ﯷﯸﯹﯺﯻﯼ
Ya ce, "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai la'ananne ne."
ﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃ
"Kuma lalle a kanka akwai la'anaTa har zuwa rãnar sakamako."
ﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊ
Ya ce, "Ya Ubangijina! To, Ka yi mini jinkiri zuwa ga rãnar da ake tãyar da su."
ﰋﰌﰍﰎﰏ
Ya ce, "To, lalle kanã daga waɗanda aka yi wa jinkiri,
ﰐﰑﰒﰓﰔ
"Zuwa ga yinin lõkaci sananne."
ﰕﰖﰗﰘﰙ
Ya ce, "To, inã rantsuwa da buwãyarKa, lalle, inã ɓatar da su gabã ɗaya.
ﰚﰛﰜﰝﰞ
"Fãce bãyinKa tsarkakakku daga gare su."
ﭑﭒﭓﭔﭕ
(Allah) Ya ce, "To, (wannan magana ita ce) gaskiya. Kuma gaskiya Nake faɗa."
ﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
"Lalle zã Ni cika Jahannama daga gare ka, kuma daga wanda ya bĩ ka daga gare su, gabã ɗaya"
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
Ka ce: "Bã ni tambayar ku wata ijãra, a kansa kuma bã ni daga mãsu ƙãƙalen faɗarsa."
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮ
"Shĩ (Alkur'ãn) bai zama ba fãce ambato ne ga dukan halitta."
ﭯﭰﭱﭲﭳ
"Kuma lalle zã ku san babban lãbãrinsa a bayan ɗan lõkaci."

Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers