Surah As-Saffat pdf — Sauke (Hausa)
Surah As-Saffat pdf Hausa — Sauke Surah As-Saffat Fassara. Surah As-Saffat (Meccan) 182 Aya.
Related
- Surah As-Saffat FassaraHausa
- Surah As-Saffat mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah As-Saffat

ﭑﭒﭓ
37:1
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
ﭔﭕﭖ
37:2
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
ﭗﭘﭙ
37:3
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
ﭚﭛﭜﭝ
37:4
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥ
37:5
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
37:6
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
37:7
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼ
37:8
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
ﭽﭾﭿﮀﮁﮂ
37:9
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
37:10
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
ﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘ
37:11
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
ﮙﮚﮛﮜ
37:12
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
ﮝﮞﮟﮠﮡ
37:13
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
ﮢﮣﮤﮥﮦ
37:14
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
ﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
37:15
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
37:16
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
ﯗﯘﯙ
37:17
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
ﯚﯛﯜﯝﯞ
37:18
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
37:19
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
ﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
37:20
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
37:21
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
ﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
37:22
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
ﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅ
37:23
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
ﰆﰇﰈﰉﰊ
37:24
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
ﭑﭒﭓﭔﭕ
37:25
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
ﭖﭗﭘﭙﭚ
37:26
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
ﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
37:27
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
ﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧ
37:28
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
ﭨﭩﭪﭫﭬﭭ
37:29
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
ﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹ
37:30
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
37:31
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
ﮂﮃﮄﮅﮆ
37:32
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
ﮇﮈﮉﮊﮋﮌ
37:33
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
ﮍﮎﮏﮐﮑ
37:34
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
ﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
37:35
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
37:36
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
37:37
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
ﮪﮫﮬﮭﮮ
37:38
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
ﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
37:39
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
ﯗﯘﯙﯚﯛ
37:40
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﯜﯝﯞﯟﯠ
37:41
Waɗannan sunã da abinci sananne.
ﯡﯢﯣﯤ
37:42
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
ﯥﯦﯧﯨ
37:43
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
ﯩﯪﯫﯬ
37:44
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲ
37:45
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
ﯳﯴﯵﯶ
37:46
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
ﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾ
37:47
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
ﯿﰀﰁﰂﰃ
37:48
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
ﰄﰅﰆﰇ
37:49
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
ﰈﰉﰊﰋﰌﰍ
37:50
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
ﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕ
37:51
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
ﭑﭒﭓﭔﭕ
37:52
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
ﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
37:53
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
ﭞﭟﭠﭡﭢ
37:54
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
37:55
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮ
37:56
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
ﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵ
37:57
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
ﭶﭷﭸﭹ
37:58
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
37:59
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
ﮁﮂﮃﮄﮅﮆ
37:60
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
ﮇﮈﮉﮊﮋ
37:61
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒ
37:62
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
ﮓﮔﮕﮖﮗ
37:63
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞ
37:64
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
ﮟﮠﮡﮢﮣ
37:65
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
37:66
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
37:67
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
ﯔﯕﯖﯗﯘﯙ
37:68
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
ﯚﯛﯜﯝﯞ
37:69
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
ﯟﯠﯡﯢﯣ
37:70
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
37:71
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
ﯪﯫﯬﯭﯮ
37:72
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
37:73
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
ﯵﯶﯷﯸﯹ
37:74
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿ
37:75
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
ﰀﰁﰂﰃﰄﰅ
37:76
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
ﭑﭒﭓﭔﭕ
37:77
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
ﭖﭗﭘﭙﭚ
37:78
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
ﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
37:79
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
ﭡﭢﭣﭤﭥ
37:80
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭦﭧﭨﭩﭪ
37:81
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
ﭫﭬﭭﭮ
37:82
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
ﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
37:83
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
37:84
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
37:85
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
ﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
37:86
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
ﮈﮉﮊﮋﮌ
37:87
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
ﮍﮎﮏﮐﮑ
37:88
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
ﮒﮓﮔﮕ
37:89
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
ﮖﮗﮘﮙ
37:90
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
37:91
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
ﮡﮢﮣﮤﮥ
37:92
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
ﮦﮧﮨﮩﮪ
37:93
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
ﮫﮬﮭﮮ
37:94
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
ﮯﮰﮱﯓﯔ
37:95
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
ﯕﯖﯗﯘﯙ
37:96
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
ﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
37:97
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
ﯢﯣﯤﯥﯦﯧ
37:98
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
ﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮ
37:99
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
37:100
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
ﯵﯶﯷﯸ
37:101
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
ﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕ
37:102
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
ﭑﭒﭓﭔﭕ
37:103
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
ﭖﭗﭘﭙ
37:104
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
ﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢ
37:105
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
37:106
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
ﭩﭪﭫﭬ
37:107
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
ﭭﭮﭯﭰﭱ
37:108
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
ﭲﭳﭴﭵ
37:109
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
ﭶﭷﭸﭹ
37:110
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭺﭻﭼﭽﭾ
37:111
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
ﭿﮀﮁﮂﮃﮄ
37:112
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐ
37:113
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
37:114
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
37:115
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
ﮝﮞﮟﮠﮡ
37:116
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
ﮢﮣﮤﮥ
37:117
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
ﮦﮧﮨﮩ
37:118
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
ﮪﮫﮬﮭﮮ
37:119
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
ﮯﮰﮱﯓﯔ
37:120
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
ﯕﯖﯗﯘﯙ
37:121
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﯚﯛﯜﯝﯞ
37:122
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
ﯟﯠﯡﯢﯣ
37:123
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
37:124
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯ
37:125
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
ﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
37:126
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
ﭑﭒﭓﭔ
37:127
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
ﭕﭖﭗﭘﭙ
37:128
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﭚﭛﭜﭝﭞ
37:129
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
ﭟﭠﭡﭢﭣ
37:130
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
ﭤﭥﭦﭧﭨ
37:131
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭩﭪﭫﭬﭭ
37:132
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
ﭮﭯﭰﭱﭲ
37:133
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
ﭳﭴﭵﭶﭷ
37:134
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
ﭸﭹﭺﭻﭼ
37:135
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
ﭽﭾﭿﮀ
37:136
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
ﮁﮂﮃﮄﮅ
37:137
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
ﮆﮇﮈﮉﮊ
37:138
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
ﮋﮌﮍﮎﮏ
37:139
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
ﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
37:140
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
ﮖﮗﮘﮙﮚ
37:141
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
ﮛﮜﮝﮞﮟ
37:142
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
ﮠﮡﮢﮣﮤﮥ
37:143
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
37:144
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
37:145
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
ﯔﯕﯖﯗﯘﯙ
37:146
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
ﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
37:147
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
ﯡﯢﯣﯤﯥ
37:148
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫ
37:149
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲ
37:150
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
ﯳﯴﯵﯶﯷﯸ
37:151
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
ﯹﯺﯻﯼﯽ
37:152
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
ﯾﯿﰀﰁﰂ
37:153
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
ﭑﭒﭓﭔﭕ
37:154
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
ﭖﭗﭘ
37:155
Shin, bã ku tunãni?
ﭙﭚﭛﭜﭝ
37:156
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
37:157
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
ﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
37:158
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
ﭰﭱﭲﭳﭴ
37:159
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
ﭵﭶﭷﭸﭹ
37:160
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﭺﭻﭼﭽ
37:161
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
ﭾﭿﮀﮁﮂ
37:162
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
37:163
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
ﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏ
37:164
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
ﮐﮑﮒﮓ
37:165
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
ﮔﮕﮖﮗ
37:166
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
ﮘﮙﮚﮛ
37:167
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
37:168
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
ﮣﮤﮥﮦﮧ
37:169
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
ﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
37:170
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
37:171
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
ﯕﯖﯗﯘ
37:172
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
ﯙﯚﯛﯜﯝ
37:173
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
ﯞﯟﯠﯡﯢ
37:174
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
ﯣﯤﯥﯦ
37:175
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
ﯧﯨﯩ
37:176
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰ
37:177
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
ﯱﯲﯳﯴﯵ
37:178
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
ﯶﯷﯸﯹ
37:179
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀ
37:180
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
ﰁﰂﰃﰄ
37:181
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
ﰅﰆﰇﰈﰉ
37:182
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
Al-Kur'ani
Wednesday, September 9, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







