Surah As-Saffat
PDF —
Built right in your browser — download starts automatically
Surah As-Saffat pdf — Sauke (Hausa)
Surah As-Saffat pdf Hausa — Sauke Surah As-Saffat Fassara. As-Saffat (Meccan) 182 Aya.
Related
- As-Saffat FassaraHausa
- As-Saffat mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah As-Saffat

ﭑﭒﭓ
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
ﭔﭕﭖ
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
ﭗﭘﭙ
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
ﭚﭛﭜﭝ
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥ
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼ
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
ﭽﭾﭿﮀﮁﮂ
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
ﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘ
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
ﮙﮚﮛﮜ
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
ﮝﮞﮟﮠﮡ
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
ﮢﮣﮤﮥﮦ
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
ﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
ﯗﯘﯙ
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
ﯚﯛﯜﯝﯞ
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
ﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
ﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
ﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅ
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
ﰆﰇﰈﰉﰊ
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
ﭑﭒﭓﭔﭕ
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
ﭖﭗﭘﭙﭚ
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
ﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
ﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧ
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
ﭨﭩﭪﭫﭬﭭ
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
ﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹ
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
ﮂﮃﮄﮅﮆ
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
ﮇﮈﮉﮊﮋﮌ
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
ﮍﮎﮏﮐﮑ
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
ﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
ﮪﮫﮬﮭﮮ
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
ﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
ﯗﯘﯙﯚﯛ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﯜﯝﯞﯟﯠ
Waɗannan sunã da abinci sananne.
ﯡﯢﯣﯤ
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
ﯥﯦﯧﯨ
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
ﯩﯪﯫﯬ
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲ
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
ﯳﯴﯵﯶ
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
ﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾ
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
ﯿﰀﰁﰂﰃ
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
ﰄﰅﰆﰇ
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
ﰈﰉﰊﰋﰌﰍ
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
ﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕ
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
ﭑﭒﭓﭔﭕ
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
ﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
ﭞﭟﭠﭡﭢ
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮ
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
ﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵ
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
ﭶﭷﭸﭹ
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
ﮁﮂﮃﮄﮅﮆ
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
ﮇﮈﮉﮊﮋ
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒ
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
ﮓﮔﮕﮖﮗ
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞ
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
ﮟﮠﮡﮢﮣ
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
ﯔﯕﯖﯗﯘﯙ
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
ﯚﯛﯜﯝﯞ
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
ﯟﯠﯡﯢﯣ
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
ﯪﯫﯬﯭﯮ
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
ﯵﯶﯷﯸﯹ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿ
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
ﰀﰁﰂﰃﰄﰅ
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
ﭑﭒﭓﭔﭕ
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
ﭖﭗﭘﭙﭚ
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
ﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
ﭡﭢﭣﭤﭥ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭦﭧﭨﭩﭪ
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
ﭫﭬﭭﭮ
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
ﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
ﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
ﮈﮉﮊﮋﮌ
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
ﮍﮎﮏﮐﮑ
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
ﮒﮓﮔﮕ
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
ﮖﮗﮘﮙ
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
ﮡﮢﮣﮤﮥ
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
ﮦﮧﮨﮩﮪ
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
ﮫﮬﮭﮮ
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
ﮯﮰﮱﯓﯔ
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
ﯕﯖﯗﯘﯙ
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
ﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
ﯢﯣﯤﯥﯦﯧ
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
ﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮ
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
ﯵﯶﯷﯸ
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
ﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕ
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
ﭑﭒﭓﭔﭕ
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
ﭖﭗﭘﭙ
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
ﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢ
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
ﭩﭪﭫﭬ
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
ﭭﭮﭯﭰﭱ
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
ﭲﭳﭴﭵ
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
ﭶﭷﭸﭹ
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭺﭻﭼﭽﭾ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
ﭿﮀﮁﮂﮃﮄ
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐ
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
ﮝﮞﮟﮠﮡ
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
ﮢﮣﮤﮥ
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
ﮦﮧﮨﮩ
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
ﮪﮫﮬﮭﮮ
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
ﮯﮰﮱﯓﯔ
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
ﯕﯖﯗﯘﯙ
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﯚﯛﯜﯝﯞ
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
ﯟﯠﯡﯢﯣ
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯ
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
ﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
ﭑﭒﭓﭔ
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
ﭕﭖﭗﭘﭙ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﭚﭛﭜﭝﭞ
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
ﭟﭠﭡﭢﭣ
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
ﭤﭥﭦﭧﭨ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
ﭩﭪﭫﭬﭭ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
ﭮﭯﭰﭱﭲ
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
ﭳﭴﭵﭶﭷ
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
ﭸﭹﭺﭻﭼ
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
ﭽﭾﭿﮀ
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
ﮁﮂﮃﮄﮅ
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
ﮆﮇﮈﮉﮊ
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
ﮋﮌﮍﮎﮏ
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
ﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
ﮖﮗﮘﮙﮚ
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
ﮛﮜﮝﮞﮟ
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
ﮠﮡﮢﮣﮤﮥ
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
ﯔﯕﯖﯗﯘﯙ
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
ﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
ﯡﯢﯣﯤﯥ
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫ
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲ
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
ﯳﯴﯵﯶﯷﯸ
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
ﯹﯺﯻﯼﯽ
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
ﯾﯿﰀﰁﰂ
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
ﭑﭒﭓﭔﭕ
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
ﭖﭗﭘ
Shin, bã ku tunãni?
ﭙﭚﭛﭜﭝ
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
ﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
ﭰﭱﭲﭳﭴ
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
ﭵﭶﭷﭸﭹ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
ﭺﭻﭼﭽ
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
ﭾﭿﮀﮁﮂ
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
ﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏ
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
ﮐﮑﮒﮓ
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
ﮔﮕﮖﮗ
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
ﮘﮙﮚﮛ
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
ﮣﮤﮥﮦﮧ
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
ﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
ﯕﯖﯗﯘ
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
ﯙﯚﯛﯜﯝ
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
ﯞﯟﯠﯡﯢ
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
ﯣﯤﯥﯦ
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
ﯧﯨﯩ
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰ
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
ﯱﯲﯳﯴﯵ
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
ﯶﯷﯸﯹ
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀ
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
ﰁﰂﰃﰄ
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
ﰅﰆﰇﰈﰉ
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
Al-Kur'ani
Tuesday, August 18, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







