Surah An-Nazi'at pdf — Sauke (Hausa)
Surah An-Nazi'at pdf Hausa — Sauke Surah An-Nazi'at Fassara. Surah An-Nazi'at (Meccan) 46 Aya.
Related
- Surah An-Nazi'at FassaraHausa
- Surah An-Nazi'at mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah An-Nazi'at

ﮢﮣﮤ
79:1
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
ﮥﮦﮧ
79:2
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
ﮨﮩﮪ
79:3
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
ﮫﮬﮭ
79:4
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
ﮮﮯﮰ
79:5
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
ﮱﯓﯔﯕ
79:6
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
ﯖﯗﯘ
79:7
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
ﯙﯚﯛﯜ
79:8
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
ﯝﯞﯟ
79:9
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
ﯠﯡﯢﯣﯤﯥ
79:10
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
ﯦﯧﯨﯩﯪ
79:11
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
ﯫﯬﯭﯮﯯﯰ
79:12
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
ﯱﯲﯳﯴﯵ
79:13
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
ﯶﯷﯸﯹ
79:14
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
ﯺﯻﯼﯽﯾ
79:15
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
ﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅ
79:16
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
79:17
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
ﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
79:18
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
ﭞﭟﭠﭡﭢ
79:19
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
ﭣﭤﭥﭦ
79:20
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
ﭧﭨﭩ
79:21
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ﭪﭫﭬﭭ
79:22
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
ﭮﭯﭰ
79:23
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
ﭱﭲﭳﭴﭵ
79:24
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
ﭶﭷﭸﭹﭺﭻ
79:25
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂ
79:26
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
79:27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
ﮋﮌﮍﮎ
79:28
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
ﮏﮐﮑﮒﮓ
79:29
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
ﮔﮕﮖﮗﮘ
79:30
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
ﮙﮚﮛﮜﮝ
79:31
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
ﮞﮟﮠ
79:32
Da duwatsu, Yã kafe ta.
ﮡﮢﮣﮤ
79:33
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
ﮥﮦﮧﮨﮩ
79:34
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
ﮪﮫﮬﮭﮮﮯ
79:35
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
ﮰﮱﯓﯔﯕ
79:36
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
ﯖﯗﯘﯙ
79:37
To, amma wanda ya yi girman kai.
ﯚﯛﯜﯝ
79:38
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
ﯞﯟﯠﯡﯢ
79:39
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
ﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
79:40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
ﯭﯮﯯﯰﯱ
79:41
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
ﯲﯳﯴﯵﯶﯷ
79:42
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
ﯸﯹﯺﯻﯼ
79:43
Me ya haɗã ka da ambatonta?
ﯽﯾﯿﰀ
79:44
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
ﰁﰂﰃﰄﰅﰆ
79:45
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
ﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐ
79:46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
Al-Kur'ani
Wednesday, September 9, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







