Surah An-Nazi'at Larabci da Hausa

Karanta Surah An-Nazi'at tare da cikakkiyar fassarar Hausa da sauti. Fassara aya bayan aya. (46 Aya — مكية). An-Nazi'at Saurara, An-Nazi'at Fassara, An-Nazi'at mp3, An-Nazi'at pdf.

Karanta da Saurara Surah An-Nazi'at

🎧 Aya
M Mishary Rashid Alafasy
M Mahmoud Khalil Al-Husary
A Abdurrahman As-Sudais
M Mohamed Siddiq Al-Minshawi
A Abdul Basit Abdul Samad
A Ali Al-Hudhaify
A Ahmed ibn Ali al-Ajamy
A Abu Bakr Ash-Shaatree
M Muhammad Ayyoub
A Abdullah Basfar
A Abdullah Al-Juhani
M Maher Al Muaiqly
x1
وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا ۝١
📖 Fassara Aya 1
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا ۝٢
📖 Fassara Aya 2
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا ۝٣
📖 Fassara Aya 3
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا ۝٤
📖 Fassara Aya 4
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا ۝٥
📖 Fassara Aya 5
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ ۝٦
📖 Fassara Aya 6
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ ۝٧
📖 Fassara Aya 7
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ ۝٨
📖 Fassara Aya 8
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ ۝٩
📖 Fassara Aya 9
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ ۝١٠
📖 Fassara Aya 10
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةً ۝١١
📖 Fassara Aya 11
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ ۝١٢
📖 Fassara Aya 12
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ ۝١٣
📖 Fassara Aya 13
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِ ۝١٤
📖 Fassara Aya 14
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ ۝١٥
📖 Fassara Aya 15
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى ۝١٦
📖 Fassara Aya 16
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ ۝١٧
📖 Fassara Aya 17
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰ أَن تَزَكَّىٰ ۝١٨
📖 Fassara Aya 18
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ۝١٩
📖 Fassara Aya 19
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ ۝٢٠
📖 Fassara Aya 20
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ۝٢١
📖 Fassara Aya 21
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ۝٢٢
📖 Fassara Aya 22
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ۝٢٣
📖 Fassara Aya 23
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ ۝٢٤
📖 Fassara Aya 24
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ ۝٢٥
📖 Fassara Aya 25
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰ ۝٢٦
📖 Fassara Aya 26
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا ۝٢٧
📖 Fassara Aya 27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا ۝٢٨
📖 Fassara Aya 28
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا ۝٢٩
📖 Fassara Aya 29
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا ۝٣٠
📖 Fassara Aya 30
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا ۝٣١
📖 Fassara Aya 31
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا ۝٣٢
📖 Fassara Aya 32
Da duwatsu, Yã kafe ta.
مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ ۝٣٣
📖 Fassara Aya 33
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ ۝٣٤
📖 Fassara Aya 34
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ مَا سَعَىٰ ۝٣٥
📖 Fassara Aya 35
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ ۝٣٦
📖 Fassara Aya 36
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ ۝٣٧
📖 Fassara Aya 37
To, amma wanda ya yi girman kai.
وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا ۝٣٨
📖 Fassara Aya 38
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ ۝٣٩
📖 Fassara Aya 39
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ ۝٤٠
📖 Fassara Aya 40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ ۝٤١
📖 Fassara Aya 41
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا ۝٤٢
📖 Fassara Aya 42
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَا ۝٤٣
📖 Fassara Aya 43
Me ya haɗã ka da ambatonta?
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَاهَا ۝٤٤
📖 Fassara Aya 44
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَا ۝٤٥
📖 Fassara Aya 45
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا ۝٤٦
📖 Fassara Aya 46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
← 78 An-Nazi'at (79/114) 80 →
Karatu Surah An-Nazi'at Hausa – Fassara da Audio

79النازعات An-Nazi'at 📚 46 Aya مكية



Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers