Surah Ad-Duha
11 Aya · Meccan · Hausa
bismillah
ﮉﮊ
Inã rantsuwa da hantsi.
ﮋﮌﮍﮎ
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
ﮛﮜﮝﮞﮟ
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
ﮠﮡﮢﮣﮤ
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
ﮥﮦﮧﮨ
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
ﮩﮪﮫﮬ
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
ﮭﮮﮯﮰﮱ
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
ﯓﯔﯕﯖﯗ
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
ﯘﯙﯚﯛﯜ
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).

Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers