Surah Al-Layl
21 Aya · Meccan · Hausa
bismillah
ﮡﮢﮣﮤ
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
ﮥﮦﮧﮨ
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
ﮩﮪﮫﮬﮭ
Da abin da ya halitta namiji da mace.
ﮮﮯﮰﮱ
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
ﯓﯔﯕﯖﯗ
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
ﯘﯙﯚ
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
ﯛﯜﯝ
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
ﯞﯟﯠﯡﯢ
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
ﯣﯤﯥ
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
ﭑﭒﭓ
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
ﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚ
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
ﭛﭜﭝﭞ
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
ﭟﭠﭡﭢﭣ
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
ﭤﭥﭦﭧ
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
ﭨﭩﭪﭫﭬ
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
ﭭﭮﭯﭰ
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
ﭱﭲﭳ
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
ﭴﭵﭶﭷﭸ
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅ
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
ﮆﮇﮈ
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).

Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers