Surah Al-Qalam pdf — Sauke (Hausa)
Surah Al-Qalam pdf Hausa — Sauke Surah Al-Qalam Fassara. Surah Al-Qalam (Meccan) 52 Aya.
Related
- Surah Al-Qalam FassaraHausa
- Surah Al-Qalam mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah Al-Qalam

ﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
68:1
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
68:2
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
68:3
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
ﮛﮜﮝﮞﮟ
68:4
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
ﮠﮡﮢ
68:5
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
ﮣﮤﮥ
68:6
Ga wanenku haukã take.
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱ
68:7
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
ﯓﯔﯕﯖ
68:8
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
ﯗﯘﯙﯚﯛ
68:9
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
68:10
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
ﯢﯣﯤﯥ
68:11
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
ﯦﯧﯨﯩﯪ
68:12
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
ﯫﯬﯭﯮﯯ
68:13
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
ﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
68:14
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
ﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
68:15
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
ﯾﯿﰀﰁ
68:16
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛ
68:17
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
ﭜﭝﭞ
68:18
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
ﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
68:19
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
ﭧﭨﭩ
68:20
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
ﭪﭫﭬ
68:21
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
68:22
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
ﭵﭶﭷﭸ
68:23
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
68:24
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
ﮀﮁﮂﮃﮄ
68:25
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
68:26
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
ﮋﮌﮍﮎ
68:27
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
68:28
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝ
68:29
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
ﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
68:30
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
68:31
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
ﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕ
68:32
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
ﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
68:33
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
ﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧ
68:34
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
ﯨﯩﯪﯫ
68:35
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
ﯬﯭﯮﯯﯰ
68:36
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
ﯱﯲﯳﯴﯵﯶ
68:37
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
ﯷﯸﯹﯺﯻﯼ
68:38
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
ﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
68:39
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
ﰊﰋﰌﰍﰎ
68:40
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
ﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕﰖﰗ
68:41
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
ﰘﰙﰚﰛﰜﰝﰞﰟﰠﰡ
68:42
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
68:43
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩ
68:44
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
68:45
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
68:46
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
68:47
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
ﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
68:48
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
ﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
68:49
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
ﮖﮗﮘﮙﮚﮛ
68:50
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨ
68:51
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
ﮩﮪﮫﮬﮭﮮ
68:52
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
Al-Kur'ani
Wednesday, September 9, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







