Surah Al-Qalam
PDF —
Built right in your browser — download starts automatically
Surah Al-Qalam pdf — Sauke (Hausa)
Surah Al-Qalam pdf Hausa — Sauke Surah Al-Qalam Fassara. Al-Qalam (Meccan) 52 Aya.
Related
- Al-Qalam FassaraHausa
- Al-Qalam mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah Al-Qalam

ﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
ﮛﮜﮝﮞﮟ
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
ﮠﮡﮢ
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
ﮣﮤﮥ
Ga wanenku haukã take.
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱ
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
ﯓﯔﯕﯖ
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
ﯗﯘﯙﯚﯛ
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
ﯢﯣﯤﯥ
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
ﯦﯧﯨﯩﯪ
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
ﯫﯬﯭﯮﯯ
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
ﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
ﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
ﯾﯿﰀﰁ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛ
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
ﭜﭝﭞ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
ﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
ﭧﭨﭩ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
ﭪﭫﭬ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
ﭵﭶﭷﭸ
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
ﮀﮁﮂﮃﮄ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
ﮋﮌﮍﮎ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
ﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
ﮪﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕ
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
ﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
ﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
ﯨﯩﯪﯫ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
ﯬﯭﯮﯯﯰ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
ﯱﯲﯳﯴﯵﯶ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
ﯷﯸﯹﯺﯻﯼ
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
ﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
ﰊﰋﰌﰍﰎ
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
ﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕﰖﰗ
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
ﰘﰙﰚﰛﰜﰝﰞﰟﰠﰡ
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩ
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
ﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
ﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
ﮖﮗﮘﮙﮚﮛ
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨ
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
ﮩﮪﮫﮬﮭﮮ
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
Al-Kur'ani
Tuesday, August 18, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







