Wadoo law takfuroona kamaa kafaroo fatakoonoona sawaaa`an falaa tattakhizoo minhum awliyaaa`a hattaa yuhaajiroo fee sabeelil laah; fa in tawallaw fa khuzoohum waqtuloohum haisu wajat tumoohum wa laa tattakhizoo minhum waliyyanw wa laa naseeraa
📖 Fassara (Da Hausa)
📖 Da Hausa
Suna gũrin ku kãfirta kamar yadda suka kãfirta, dõmin ku kasance daidai. Sabõda haka kada ku riƙi wasu masõya daga cikinsu, sai sun yõ hijira a cikin hanyar Allah. Sa'an nan idan sun jũya, to, ku kãmã su kuma ku kashe su inda duk kuka sãme su. Kuma kada ku riƙi wani masõyi daga gare su ko wani mataimaki.
يُهَاجِرُوا: Su bar garin kafirai su zo garin musulmi domin neman yardar Allah.
تَوَلَّوْا: Su juya baya daga imani da hijira.
خُذُوهُمْ: Ku kama su a matsayin fursuna.
وَلِيًّا: Abokin kusanci da taimako.
نَصِيرًا: Mai taimakon ku a kan maƙiyanku.
Tafsirin Ayar:
Munafukai suna fata ku kafirta da abin da Allah ya saukar, kamar yadda suka kafirta, domin ku zama daidai da su a cikin kafirci. Don haka, kada ku ɗauke su abokan zumunci, ko da sun bayyana imani, har sai sun yi hijira don neman yardar Allah da Manzonsa, ba don buƙatun duniya ba. Idan suka juya baya daga imani da hijira, to ku kama su a matsayin fursuna, ku kashe su a duk inda kuka same su, ko a cikin ƙasa mai tsarki (Makka) ko wajen ta. Kada ku ɗauke daga gare su wani abokin kusanci da zai taimake ku a kan al'amuranku, ko wani mai taimako da zai taimake ku a kan maƙiyanku, domin suna nuna ƙiyayya da yaudara gare ku.
Fa'idodin Darasi:
Munafukai suna ƙin imani ga musulmi, kuma suna so su juye su daga addininsu, don haka ya kamata musulmi su yi hattara da su.
Hijira a cikin hanyar Allah alama ce ta gaskiyar imani, kuma ba za a amince da mutum ba har sai ya nuna gaskiyarsa ta hanyar aiki.
Musulmi ba za su ɗauki munafukai abokan zumunci ba, kuma ba za su dogara gare su ba a kowane hali.
Tsananin hukunci ga waɗanda suka juya baya daga imani da suka ci gaba da ƙiyayya da musulmi, yana nuna muhimmancin kare addini da al'ummar musulmi.
Ayar tana ƙarfafa musulmi su kasance masu tsayin daka a kan imaninsu, kuma kada su bar munafukai su rinjaye su da yaudara.
Suna gũrin ku kãfirta kamar yadda suka kãfirta, dõmin ku kasance daidai. Sabõda haka kada ku riƙi wasu masõya daga cikinsu, sai sun yõ hijira a cikin hanyar Allah. Sa'an nan idan sun jũya, to, ku kãmã su kuma ku kashe su inda duk kuka sãme su. Kuma kada ku riƙi wani masõyi daga gare su ko wani mataimaki.
Allah bãbu abin bautawa face Shi. Lalle ne haƙĩƙa Yana tãra ku har zuwa ga Yinin ¡iyãma bãbu shakka a cikinsa. Kuma wãne ne mafi gaskiya daga Allah ga 1ãbãri.
To, mẽne ne ya sãme ku a cikin munãfukai kun zama ƙungiya biyu, alhãli kuwa Allah ne Ya mayar da su sabõda abin da suka tsirfanta? Shin, kunã nufin ku shiryar da wanda Allah Ya ɓatar ne? Kuma wanda Allah Ya ɓatar to bã zã ka sãmi wata hanya ba zuwa gare shi.
Suna gũrin ku kãfirta kamar yadda suka kãfirta, dõmin ku kasance daidai. Sabõda haka kada ku riƙi wasu masõya daga cikinsu, sai sun yõ hijira a cikin hanyar Allah. Sa'an nan idan sun jũya, to, ku kãmã su kuma ku kashe su inda duk kuka sãme su. Kuma kada ku riƙi wani masõyi daga gare su ko wani mataimaki.
Fãce dai waɗanda suke sãduwa zuwa ga wasu mutãne waɗanda a tsakãninku da su akwai alkawari, kõ kuwa waɗanda suke sun je muku (domin) ƙirãzansu sun yi ƙunci ga su yãke ku, kõ su yãƙi mutãnensu. Kuma dã Allah Yã so lalle ne, dã Yã bã su ĩko a kanku, sa'an nan, haƙĩka, su yãke ku. To, idan sun nĩsance ku sa'an nan ba su yãƙe ku ba, kuma suka jẽfa sulhu zuwa gare ku, to, Allah bai sanya wata hanya ba, a gare ku, a kansu.
Za ku sãmi wasu sunã nufin su amintar da ku kuma su amintar da mutãnensu, kõ da yaushe aka mayar da su ga fitina, sai a dulmuyã su a cikinta. To, idan ba su nĩsance ku ba, kuma sun jẽfa sulhu zuwa gare ku, kuma sun kange hannuwansu, to, ku kãmã su, kuma ku kashe su inda duk kuka kãmã su, kuma waɗannan, Mun sanya muku dalĩli bayyanannea kansu.
SurahQuran.com was founded as a humble effort to serve the Noble Book and the pure Sunnah, to invite people to Allah, and to make the religious sciences accessible according to the methodology of the Quran and Sunnah. We praise and thank Allah for His grace, and we ask Him to accept our work and make it sincere for His noble Face.