Al-Ahzab · 36/73
Fassara Rubutun sauti — Surah Al-Ahzab
وَمَا كَانَ لِمُؤْمِنٍ وَلَا مُؤْمِنَةٍ إِذَا قَضَى اللَّهُ وَرَسُولُهُ أَمْرًا أَن يَكُونَ لَهُمُ الْخِيَرَةُ مِنْ أَمْرِهِمْ ۗ وَمَن يَعْصِ اللَّهَ وَرَسُولَهُ فَقَدْ ضَلَّ ضَلَالًا مُّبِينًا ۝٣٦
Wa maa kaana limu`mininw wa laa mu`minatin izaa qadal laahu wa Rasooluhooo amran ai yakoona lahumul khiyaratu min amrihim; wa mai ya`sil laaha wa Rasoolahoo faqad dalla dalaalam mubeenaa
📖 Da Hausa
Kuma ba ya halatta ga mũmini kuma haka ga mũmina, a lõkacin da Allah da Manzonsa Ya hukunta wani umurni, wani zãɓi daga al'amarinsu ya kasance a gare su. Kuma wanda ya sãɓã wa Allah da ManzonSa, to, yã ɓace, ɓacẽwa bayyananna.

🎧 Saurara
📜

Fassara — Tafsir

Ma’anonin Kalmomi:

  • Qaḍā: Ya yanke hukunci ko ya ƙaddara.
  • Al-Khiyarah: Zaɓi ko son rai na karɓa ko ƙi.
  • Ḍalāl: Bata ko ɓacewa daga hanya madaidaiciya.

Tafsirin Ayar:

Ba ya dace da wani mumini namiji ko mace, idan Allah da Manzonsa (SAW) sun yanke hukunci a kan wani al’amari, su kasance da zaɓi na daban daga abin da Allah da Manzonsa suka yanke. Wato, ba su da ikon karɓa ko ƙi abin da Allah da Manzonsa suka ƙaddara, amma wajibi ne su bi da mika wuya ga hukuncin Allah da Manzonsa cikin gaba ɗaya. Wannan ayar ta zo ne a kan labarin Zainab bint Jahsh (RA) da auren da Allah ya umarce ta da shi da Zaid bin Harithah (RA), inda take da ɗan ƙin yarda, sai Allah ya bayyana cewa babu wani zaɓi ga mumini idan Allah da Manzonsa sun yanke hukunci. Duk wanda ya saba wa umurnin Allah da Manzonsa, to ya ɓace ɓacewa bayyananna, kuma ya nisa daga hanyar gaskiya da adalci.

Fa’idojin Ayar:

  1. Imani na gaskiya yana buƙatar cikakken mika wuya ga hukuncin Allah da Manzonsa (SAW), ba tare da ƙin yarda ko zaɓi na son rai ba.
  2. Musulmi namiji ko mace ba su da wani zaɓi idan Allah da Manzonsa sun yanke hukunci, domin hukuncinsu shi ne mafi alheri da hikima.
  3. Saba wa umurnin Allah da Manzonsa alama ce ta ɓata bayyananna, wadda ke kaiwa ga hasara a duniya da lahira.
  4. Ayar tana koyar da cewa biyayya ga Allah da Manzonsa ita ce tushen nasara da saukin al’amura, kuma tana nuna girman darajar muminai a gaban Allah.
  5. Ta ƙarfafa muminai su yarda da hukuncin Allah da Manzonsa cikin natsuwa da imani, domin sanin cewa Allah ne Mafi sanin abin da ke da alheri ga bayinsa.


📜 Aya 34-38 — Surah Al-Ahzab

34وَاذْكُرْنَ مَا يُتْلَىٰ فِي بُيُوتِكُنَّ مِنْ آيَاتِ اللَّهِ وَالْحِكْمَةِ ۚ إِنَّ اللَّهَ كَانَ لَطِيفًا خَبِيرًا
Kuma ku tuna abin da ake karantawa a cikin ɗãkunanku daga ãyõyin Allah da hukunci. Lalle Allah Yã kasance Mai tausasãwa Mai labartawa.
35إِنَّ الْمُسْلِمِينَ وَالْمُسْلِمَاتِ وَالْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ وَالْقَانِتِينَ وَالْقَانِتَاتِ وَالصَّادِقِينَ وَالصَّادِقَاتِ وَالصَّابِرِينَ وَالصَّابِرَاتِ وَالْخَاشِعِينَ وَالْخَاشِعَاتِ وَالْمُتَصَدِّقِينَ وَالْمُتَصَدِّقَاتِ وَالصَّائِمِينَ وَالصَّائِمَاتِ وَالْحَافِظِينَ فُرُوجَهُمْ وَالْحَافِظَاتِ وَالذَّاكِرِينَ اللَّهَ كَثِيرًا وَالذَّاكِرَاتِ أَعَدَّ اللَّهُ لَهُم مَّغْفِرَةً وَأَجْرًا عَظِيمًا
Lalle, Musulmi maza da Musulmi mãtã da muminai maza da muminai mãtã, da mãsu tawãli'u maza da mãsu tawãlĩu mãtãda mãsu gaskiya maza da mãsu gaskiya mãtã, da mãsu haƙuri maza da mãsu haƙuri mãtã, da mãsu tsõron Allah maza da mãsu tsõron Allah mãtã, da mãsu sadaka maza da mãsu sadaka mãtã, da mãsu azumi maza da mãsu azumi mãtã da mãsu tsare farjõjinsu maza da mãsu tsare farjõjinsu mãtã, da mãsu ambaton Allah da yawa maza da mãsu ambatonsa mãtã, Allah Ya yi musu tattalin wata gãfara da wani sakamako mai girma.
36وَمَا كَانَ لِمُؤْمِنٍ وَلَا مُؤْمِنَةٍ إِذَا قَضَى اللَّهُ وَرَسُولُهُ أَمْرًا أَن يَكُونَ لَهُمُ الْخِيَرَةُ مِنْ أَمْرِهِمْ ۗ وَمَن يَعْصِ اللَّهَ وَرَسُولَهُ فَقَدْ ضَلَّ ضَلَالًا مُّبِينًا
Kuma ba ya halatta ga mũmini kuma haka ga mũmina, a lõkacin da Allah da Manzonsa Ya hukunta wani umurni, wani zãɓi daga al'amarinsu ya kasance a gare su. Kuma wanda ya sãɓã wa Allah da ManzonSa, to, yã ɓace, ɓacẽwa bayyananna.
37وَإِذْ تَقُولُ لِلَّذِي أَنْعَمَ اللَّهُ عَلَيْهِ وَأَنْعَمْتَ عَلَيْهِ أَمْسِكْ عَلَيْكَ زَوْجَكَ وَاتَّقِ اللَّهَ وَتُخْفِي فِي نَفْسِكَ مَا اللَّهُ مُبْدِيهِ وَتَخْشَى النَّاسَ وَاللَّهُ أَحَقُّ أَن تَخْشَاهُ ۖ فَلَمَّا قَضَىٰ زَيْدٌ مِّنْهَا وَطَرًا زَوَّجْنَاكَهَا لِكَيْ لَا يَكُونَ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ حَرَجٌ فِي أَزْوَاجِ أَدْعِيَائِهِمْ إِذَا قَضَوْا مِنْهُنَّ وَطَرًا ۚ وَكَانَ أَمْرُ اللَّهِ مَفْعُولًا
Kuma a lõkacin da kake cẽwa ga wanda Allah Ya yi ni'ima a gare shi kai kuma ka yi ni'ima a gare shi, "Ka riƙe mãtarka, kuma ka bi Allah da taƙawa," kuma kana ɓõyẽwa a cikin ranka abin da Allah zai bayyana shi, kanã tsõron mutãne, alhãli kuwa Allah ne Mafi cancantar ka ji tsõronSa. to a lõkacin da zaidu ya ƙãre bukãtarsa daga gare ta, Mun aurar da kai ita, dõmin kada wani ƙunci ya kasance a kan mũminai a cikin (auren mãtan) ɗiyan hankãkarsu, idan sun ƙãre bukãta daga gare su. Kuma umurnin Allah yã kasance abin aikatãwa.
38مَّا كَانَ عَلَى النَّبِيِّ مِنْ حَرَجٍ فِيمَا فَرَضَ اللَّهُ لَهُ ۖ سُنَّةَ اللَّهِ فِي الَّذِينَ خَلَوْا مِن قَبْلُ ۚ وَكَانَ أَمْرُ اللَّهِ قَدَرًا مَّقْدُورًا
Wani ƙunci bai kasance a kan Annabi ba ga abin da Allah Ya faralta a kansa, a kan ƙã'idar, Allah a cikin (Annabãwa) waɗanda suka shige daga gabãninsa. Kuma umurnin Allah yã kasance abin ƙaddarãwa tabbatacce.
Al-AhzabJerin Alqur'ani
73Aya
MedinanRevelation
36Aya

Fassara — Al-Ahzab 36

Surah Al-Ahzab Aya 36 - Karatu, Saurara, Fassara, Hausa : Kuma ba ya halatta ga mũmini kuma haka ga mũmina,…

Surah Aya 36/73 — Surah Al-Ahzab الأحزاب (Medinan). Karatu Saurara Fassara (Hausa). Saurara: Surah Al-Ahzab Saurara, Surah Al-Ahzab Fassara, Surah Al-Ahzab mp3, Surah Al-Ahzab pdf. Aya 34–38. Da Hausa: العربية.




Al-Kur'ani


Tuesday, September 8, 2026

Don't forget us in your sincere prayers