📖 0/604 shafuka an karanta
📄 591
Surah At-Tariq
bismillah
وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ  ۝١ وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ  ۝٢ ٱلنَّجۡمُ ٱلثَّاقِبُ  ۝٣ إِن كُلُّ نَفۡسٍ لَّمَّا عَلَيۡهَا حَافِظٌ  ۝٤ فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ  ۝٥ خُلِقَ مِن مَّآءٍ دَافِقٍ  ۝٦ يَخۡرُجُ مِنۢ بَيۡنِ ٱلصُّلۡبِ وَٱلتَّرَآئِبِ  ۝٧ إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٌ  ۝٨ يَوۡمَ تُبۡلَى ٱلسَّرَآئِرُ  ۝٩ فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٍ وَلَا نَاصِرٍ  ۝١٠ وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجۡعِ  ۝١١ وَٱلۡأَرۡضِ ذَاتِ ٱلصَّدۡعِ  ۝١٢ إِنَّهُۥ لَقَوۡلٌ فَصۡلٌ  ۝١٣ وَمَا هُوَ بِٱلۡهَزۡلِ  ۝١٤ إِنَّهُمۡ يَكِيدُونَ كَيۡدًا  ۝١٥ وَأَكِيدُ كَيۡدًا  ۝١٦ فَمَهِّلِ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَمۡهِلۡهُمۡ رُوَيۡدَۢا  ۝١٧
Surah Al-A'la
bismillah
سَبِّحِ ٱسۡمَ رَبِّكَ ٱلۡأَعۡلَى  ۝١ ٱلَّذِي خَلَقَ فَسَوَّىٰ  ۝٢ وَٱلَّذِي قَدَّرَ فَهَدَىٰ  ۝٣ وَٱلَّذِيٓ أَخۡرَجَ ٱلۡمَرۡعَىٰ  ۝٤ فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحۡوَىٰ  ۝٥ سَنُقۡرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ  ۝٦ إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ  ۝٧ وَنُيَسِّرُكَ لِلۡيُسۡرَىٰ  ۝٨ فَذَكِّرۡ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكۡرَىٰ  ۝٩ سَيَذَّكَّرُ مَن يَخۡشَىٰ  ۝١٠ وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلۡأَشۡقَى  ۝١١ ٱلَّذِي يَصۡلَى ٱلنَّارَ ٱلۡكُبۡرَىٰ  ۝١٢ ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحۡيَىٰ  ۝١٣ قَدۡ أَفۡلَحَ مَن تَزَكَّىٰ  ۝١٤ وَذَكَرَ ٱسۡمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ  ۝١٥
Surah At-Tariq
bismillah
86:1
وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ  ۝١
Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.
86:2
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ  ۝٢
To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?
86:3
ٱلنَّجۡمُ ٱلثَّاقِبُ  ۝٣
Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.
86:4
إِن كُلُّ نَفۡسٍ لَّمَّا عَلَيۡهَا حَافِظٌ  ۝٤
Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.
86:5
فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ  ۝٥
To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?
86:6
خُلِقَ مِن مَّآءٍ دَافِقٍ  ۝٦
An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.
86:7
يَخۡرُجُ مِنۢ بَيۡنِ ٱلصُّلۡبِ وَٱلتَّرَآئِبِ  ۝٧
Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.
86:8
إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٌ  ۝٨
Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.
86:9
يَوۡمَ تُبۡلَى ٱلسَّرَآئِرُ  ۝٩
Rãnar da ake jarrabawar asirai.
86:10
فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٍ وَلَا نَاصِرٍ  ۝١٠
Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).
86:11
وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجۡعِ  ۝١١
Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.
86:12
وَٱلۡأَرۡضِ ذَاتِ ٱلصَّدۡعِ  ۝١٢
Da ƙasa ma'abũciyar tsãgẽwa,
86:13
إِنَّهُۥ لَقَوۡلٌ فَصۡلٌ  ۝١٣
Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki
86:14
وَمَا هُوَ بِٱلۡهَزۡلِ  ۝١٤
Kuma shĩ bã bananci bane
86:15
إِنَّهُمۡ يَكِيدُونَ كَيۡدًا  ۝١٥
Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.
86:16
وَأَكِيدُ كَيۡدًا  ۝١٦
Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.
86:17
فَمَهِّلِ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَمۡهِلۡهُمۡ رُوَيۡدَۢا  ۝١٧
Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.
Surah Al-A'la
bismillah
87:1
سَبِّحِ ٱسۡمَ رَبِّكَ ٱلۡأَعۡلَى  ۝١
Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.
87:2
ٱلَّذِي خَلَقَ فَسَوَّىٰ  ۝٢
Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.
87:3
وَٱلَّذِي قَدَّرَ فَهَدَىٰ  ۝٣
Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).
87:4
وَٱلَّذِيٓ أَخۡرَجَ ٱلۡمَرۡعَىٰ  ۝٤
Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.
87:5
فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحۡوَىٰ  ۝٥
Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.
87:6
سَنُقۡرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ  ۝٦
Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.
87:7
إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ  ۝٧
Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.
87:8
وَنُيَسِّرُكَ لِلۡيُسۡرَىٰ  ۝٨
Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.
87:9
فَذَكِّرۡ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكۡرَىٰ  ۝٩
Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.
87:10
سَيَذَّكَّرُ مَن يَخۡشَىٰ  ۝١٠
Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.
87:11
وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلۡأَشۡقَى  ۝١١
Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,
87:12
ٱلَّذِي يَصۡلَى ٱلنَّارَ ٱلۡكُبۡرَىٰ  ۝١٢
Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.
87:13
ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحۡيَىٰ  ۝١٣
Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.
87:14
قَدۡ أَفۡلَحَ مَن تَزَكَّىٰ  ۝١٤
Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.
87:15
وَذَكَرَ ٱسۡمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ  ۝١٥
Kuma ya ambaci sũnan Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.


📚Juz 30 📄591 / 604



Mishary Rashid Alafasy
Mahmoud Khalil Al-Husary
Abdurrahman As-Sudais
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
Abdul Basit Abdul Samad
Ali Al-Hudhaify
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
Abu Bakr Ash-Shaatree
Muhammad Ayyoub
Abdullah Basfar
Abdullah Al-Juhani
Maher Al Muaiqly
0:00
0:00
-

Al-Kur'ani


Tuesday, September 1, 2026

Don't forget us in your sincere prayers