Wa wassainal insaana biwaalidaihi ihsaanan hamalathu ummuhoo kurhanw-wa wada`athu kurhanw wa hamluhoo wa fisaaluhoo salaasoona shahraa; hattaaa izaa balagha ashuddahoo wa balagho arba`eena sanatan qaala Rabbi aqzi`neee an ashkura ni`matakal lateee an`amta `alaiya wa `alaa waalidaiya wa an a`mala saalihan tardaahu wa aslih lee fee zurriyyatee innee tubtu ilaika wa innee minal muslimeen
📖 Fassara (Da Hausa)
📖 Da Hausa
Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu da kyautatãwa, uwarsa tã yi cikinsa wahala, kuma ta haife shi wahala. cikinsa da yãyensa watã talãtin. Har a lõkacin da ya kai ga mafi ƙarfinsa, kuma ya kai shẽkara arba'in, ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka kange nidõmin in gõde wa ni'imarKa, wadda Ka ni'imta a kaina da kuma a kan mahaifãna biyu, kuma dõmin in aikata aikin ƙwarai wanda Kake yarda da shi, kuma Ka kyautata mini a cikin zuriyata. Lalle nĩ, nã tũba zuwa gare Ka, kuma lalle ni, inã daga mãsu sallamãwa (ga umurninKa)."
أَوْزِعْنِي: Ka sa ni in himmatu da kuma a sa ni in iya.
أَشُدَّهُ: Cikakken ƙarfin jiki da hankali.
فِصَالُهُ: Yaye shi daga nono.
Tafsirin Ayar:
Mun yi wa ɗan Adam wasiyya mai ƙarfi da umarni cewa ya kyautata wa iyayensa biyu, ta hanyar yin musu biyayya da alheri a rayuwarsu da kuma bayan mutuwarsu, gwargwadon abin da ba ya saba wa Shari'a. Musamman mahaifiyarsa, domin ita ce ta ɗauke shi cikin ciki da wahala da shan wuya, kuma ta haife shi da wahala da shan wuya. Kuma tsawon lokacin ciki da kuma yaye shi daga nono duka sun kai watanni talatin. Wannan ambaton wahalhalu da mahaifiya ke sha, ba uba ba, yana nuna cewa hakkin mahaifiya a kan ɗanta ya fi na uba girma.
Har zuwa lokacin da mutum ya kai cikakken ƙarfinsa na jiki da hankali, kuma ya kai shekaru arba'in, sai ya ce: "Ya Ubangijina! Ka sa ni in iya godiya da ni'momin da ka yi mini ni da iyayena, kuma ka sa ni in yi aikin ƙwarai wanda kake yarda da shi, kuma ka kyautata mini zuriyata. Lallai ni na tuba gare Ka daga dukkan zunubaina, kuma ina cikin masu sallama wa umarninka da masu bin dokokin ka."
Fa'idodin da ake samu daga wannan ayar:
Nuna girman hakkin iyaye, musamman mahaifiya, a kan 'ya'yansu, kuma cewa kyautata musu wajibi ne a kan kowane Musulmi.
Ƙarfafa wa mutum yin addu'a ga Ubangijinsa da neman taimakonSa a kan yin ayyukan alheri da kuma kyautata zuriya.
Nuna cewa tuba gare Allah da sallama wa umarninSa su ne hanyar samun nasara da yardar Allah.
Ƙarfafa wa mutum yin godiya ga Allah a kan ni'imominSa, musamman a lokacin da ya kai shekarun balaga da cikakken hankali.
Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu da kyautatãwa, uwarsa tã yi cikinsa wahala, kuma ta haife shi wahala. cikinsa da yãyensa watã talãtin. Har a lõkacin da ya kai ga mafi ƙarfinsa, kuma ya kai shẽkara arba'in, ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka kange nidõmin in gõde wa ni'imarKa, wadda Ka ni'imta a kaina da kuma a kan mahaifãna biyu, kuma dõmin in aikata aikin ƙwarai wanda Kake yarda da shi, kuma Ka kyautata mini a cikin zuriyata. Lalle nĩ, nã tũba zuwa gare Ka, kuma lalle ni, inã daga mãsu sallamãwa (ga umurninKa)."
Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu da kyautatãwa, uwarsa tã yi cikinsa wahala, kuma ta haife shi wahala. cikinsa da yãyensa watã talãtin. Har a lõkacin da ya kai ga mafi ƙarfinsa, kuma ya kai shẽkara arba'in, ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka kange nidõmin in gõde wa ni'imarKa, wadda Ka ni'imta a kaina da kuma a kan mahaifãna biyu, kuma dõmin in aikata aikin ƙwarai wanda Kake yarda da shi, kuma Ka kyautata mini a cikin zuriyata. Lalle nĩ, nã tũba zuwa gare Ka, kuma lalle ni, inã daga mãsu sallamãwa (ga umurninKa)."
Waɗancan ne waɗanda Muke karɓa, daga gare su, mafi kyaun abin da suka aikata, kuma Muke gãfarta mafi mũnanan ayyukansum (sunã) a cikin 'yan Aljanna, a kan wa'adin gaskiya wanda suka kasance anã yi musu alkawari (da shi).
Kuma wanda ya ce wa mahaifansa biyu: "Tir gare ku! shin, kunã tsõratar da ni cẽwa zã a fitar da ni daga (kabari) ne, alhãli kuwa ƙarnõni na mutãne da yawa sun shũɗe a gabãnĩna (ba su kõmo ba)?" Kuma sũ (mahaifan) sunã nẽman Allah taimako (sunãce masa) "Kaitonka! Ka yi ĩmãni, lalle wa'adin Allah gaskiya ne." Sai shi kuma ya ce. "Wannan bã kõme ba ne fãce tãtsũniyõyin mutãnen farko."
SurahQuran.com was founded as a humble effort to serve the Noble Book and the pure Sunnah, to invite people to Allah, and to make the religious sciences accessible according to the methodology of the Quran and Sunnah. We praise and thank Allah for His grace, and we ask Him to accept our work and make it sincere for His noble Face.