La sourate An-Naziat en Haoussa

  1. mp3 sourate
  2. Plus
  3. Haoussa
Le Saint Coran | Traduction du Coran | Langue Haoussa | Sourate An-Naziat | - Nombre de versets 46 - Le numéro de la sourate dans le mushaf: 79 - La signification de la sourate en English: Those Who Tear Out.

وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا(1)

 Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا(2)

 Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا(3)

 Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا(4)

 Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا(5)

 Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ(6)

 Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ(7)

 Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ(8)

 Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ(9)

 Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ(10)

 Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةً(11)

 "Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ(12)

 Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ(13)

 To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِ(14)

 Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ(15)

 Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى(16)

 A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ(17)

 Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰ أَن تَزَكَّىٰ(18)

 "Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ(19)

 "Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ(20)

 Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ(21)

 Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ(22)

 Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ(23)

 Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ(24)

 Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ(25)

 Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰ(26)

 Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا(27)

 Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا(28)

 Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا(29)

 Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا(30)

 Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا(31)

 Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا(32)

 Da duwatsu, Yã kafe ta.

مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ(33)

 Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ(34)

 To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ مَا سَعَىٰ(35)

 Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ(36)

 Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ(37)

 To, amma wanda ya yi girman kai.

وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا(38)

 Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ(39)

 To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ(40)

 Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ(41)

 To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا(42)

 Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَا(43)

 Me ya haɗã ka da ambatonta?

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَاهَا(44)

 Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَا(45)

 Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا(46)

 Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.


Plus de sourates en Haoussa :


Al-Baqarah Al-'Imran An-Nisa'
Al-Ma'idah Yusuf Ibrahim
Al-Hijr Al-Kahf Maryam
Al-Hajj Al-Qasas Al-'Ankabut
As-Sajdah Ya Sin Ad-Dukhan
Al-Fath Al-Hujurat Qaf
An-Najm Ar-Rahman Al-Waqi'ah
Al-Hashr Al-Mulk Al-Haqqah
Al-Inshiqaq Al-A'la Al-Ghashiyah

Téléchargez la sourate avec la voix des récitants du Coran les plus célèbres :

Téléchargez le fichier mp3 de la sourate An-Naziat : choisissez le récitateur pour écouter et télécharger la sourate An-Naziat complète en haute qualité.


surah An-Naziat Ahmed El Agamy
Ahmed Al Ajmy
surah An-Naziat Bandar Balila
Bandar Balila
surah An-Naziat Khalid Al Jalil
Khalid Al Jalil
surah An-Naziat Saad Al Ghamdi
Saad Al Ghamdi
surah An-Naziat Saud Al Shuraim
Saud Al Shuraim
surah An-Naziat Abdul Basit Abdul Samad
Abdul Basit
surah An-Naziat Abdul Rashid Sufi
Abdul Rashid Sufi
surah An-Naziat Abdullah Basfar
Abdullah Basfar
surah An-Naziat Abdullah Awwad Al Juhani
Abdullah Al Juhani
surah An-Naziat Fares Abbad
Fares Abbad
surah An-Naziat Maher Al Muaiqly
Maher Al Muaiqly
surah An-Naziat Muhammad Siddiq Al Minshawi
Al Minshawi
surah An-Naziat Al Hosary
Al Hosary
surah An-Naziat Al-afasi
Mishari Al-afasi
surah An-Naziat Yasser Al Dosari
Yasser Al Dosari


Wednesday, May 15, 2024

Donnez-nous une invitation valide