Surah An-Najm with Hausa

  1. Surah mp3
  2. More
  3. Hausa
The Holy Quran | Quran translation | Language Hausa | Surah Najm | النجم - Ayat Count 62 - The number of the surah in moshaf: 53 - The meaning of the surah in English: The Star.

وَالنَّجْمِ إِذَا هَوَىٰ(1)

 Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.

مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ(2)

 Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.

وَمَا يَنطِقُ عَنِ الْهَوَىٰ(3)

 Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.

إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْيٌ يُوحَىٰ(4)

 (Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.

عَلَّمَهُ شَدِيدُ الْقُوَىٰ(5)

 (Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.

ذُو مِرَّةٍ فَاسْتَوَىٰ(6)

 Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.

وَهُوَ بِالْأُفُقِ الْأَعْلَىٰ(7)

 Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.

ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ(8)

 Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.

فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ(9)

 Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.

فَأَوْحَىٰ إِلَىٰ عَبْدِهِ مَا أَوْحَىٰ(10)

 Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).

مَا كَذَبَ الْفُؤَادُ مَا رَأَىٰ(11)

 Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.

أَفَتُمَارُونَهُ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ(12)

 Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?

وَلَقَدْ رَآهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ(13)

 Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.

عِندَ سِدْرَةِ الْمُنتَهَىٰ(14)

 A wurin da magaryar tuƙẽwa take.

عِندَهَا جَنَّةُ الْمَأْوَىٰ(15)

 A inda taken, nan Aljannar makoma take.

إِذْ يَغْشَى السِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ(16)

 Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.

مَا زَاغَ الْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ(17)

 Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.

لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ آيَاتِ رَبِّهِ الْكُبْرَىٰ(18)

 Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.

أَفَرَأَيْتُمُ اللَّاتَ وَالْعُزَّىٰ(19)

 Shin, kun ga Lãta da uzza?

وَمَنَاةَ الثَّالِثَةَ الْأُخْرَىٰ(20)

 Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?

أَلَكُمُ الذَّكَرُ وَلَهُ الْأُنثَىٰ(21)

 Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?

تِلْكَ إِذًا قِسْمَةٌ ضِيزَىٰ(22)

 Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.

إِنْ هِيَ إِلَّا أَسْمَاءٌ سَمَّيْتُمُوهَا أَنتُمْ وَآبَاؤُكُم مَّا أَنزَلَ اللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَانٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ وَمَا تَهْوَى الْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَاءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ الْهُدَىٰ(23)

 Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).

أَمْ لِلْإِنسَانِ مَا تَمَنَّىٰ(24)

 Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?

فَلِلَّهِ الْآخِرَةُ وَالْأُولَىٰ(25)

 To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).

۞ وَكَم مِّن مَّلَكٍ فِي السَّمَاوَاتِ لَا تُغْنِي شَفَاعَتُهُمْ شَيْئًا إِلَّا مِن بَعْدِ أَن يَأْذَنَ اللَّهُ لِمَن يَشَاءُ وَيَرْضَىٰ(26)

 Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.

إِنَّ الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِالْآخِرَةِ لَيُسَمُّونَ الْمَلَائِكَةَ تَسْمِيَةَ الْأُنثَىٰ(27)

 Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.

وَمَا لَهُم بِهِ مِنْ عِلْمٍ ۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ ۖ وَإِنَّ الظَّنَّ لَا يُغْنِي مِنَ الْحَقِّ شَيْئًا(28)

 Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.

فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلَّا الْحَيَاةَ الدُّنْيَا(29)

 Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).

ذَٰلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ الْعِلْمِ ۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اهْتَدَىٰ(30)

 Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.

وَلِلَّهِ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ لِيَجْزِيَ الَّذِينَ أَسَاءُوا بِمَا عَمِلُوا وَيَجْزِيَ الَّذِينَ أَحْسَنُوا بِالْحُسْنَى(31)

 Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.

الَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَائِرَ الْإِثْمِ وَالْفَوَاحِشَ إِلَّا اللَّمَمَ ۚ إِنَّ رَبَّكَ وَاسِعُ الْمَغْفِرَةِ ۚ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ الْأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌ فِي بُطُونِ أُمَّهَاتِكُمْ ۖ فَلَا تُزَكُّوا أَنفُسَكُمْ ۖ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اتَّقَىٰ(32)

 Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.

أَفَرَأَيْتَ الَّذِي تَوَلَّىٰ(33)

 Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?

وَأَعْطَىٰ قَلِيلًا وَأَكْدَىٰ(34)

 Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?

أَعِندَهُ عِلْمُ الْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىٰ(35)

 Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?

أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ(36)

 Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?

وَإِبْرَاهِيمَ الَّذِي وَفَّىٰ(37)

 Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?

أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌ وِزْرَ أُخْرَىٰ(38)

 Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.

وَأَن لَّيْسَ لِلْإِنسَانِ إِلَّا مَا سَعَىٰ(39)

 Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.

وَأَنَّ سَعْيَهُ سَوْفَ يُرَىٰ(40)

 Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.

ثُمَّ يُجْزَاهُ الْجَزَاءَ الْأَوْفَىٰ(41)

 Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?

وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ الْمُنتَهَىٰ(42)

 Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?

وَأَنَّهُ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىٰ(43)

 Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.

وَأَنَّهُ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَا(44)

 Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.

وَأَنَّهُ خَلَقَ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ(45)

 Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.

مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ(46)

 Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.

وَأَنَّ عَلَيْهِ النَّشْأَةَ الْأُخْرَىٰ(47)

 Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.

وَأَنَّهُ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ(48)

 Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.

وَأَنَّهُ هُوَ رَبُّ الشِّعْرَىٰ(49)

 Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.

وَأَنَّهُ أَهْلَكَ عَادًا الْأُولَىٰ(50)

 Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.

وَثَمُودَ فَمَا أَبْقَىٰ(51)

 Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.

وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ(52)

 Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.

وَالْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىٰ(53)

 Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.

فَغَشَّاهَا مَا غَشَّىٰ(54)

 Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ(55)

 To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?

هَٰذَا نَذِيرٌ مِّنَ النُّذُرِ الْأُولَىٰ(56)

 wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.

أَزِفَتِ الْآزِفَةُ(57)

 Makusanciya fa, tã yi kusa.

لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ اللَّهِ كَاشِفَةٌ(58)

 Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.

أَفَمِنْ هَٰذَا الْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ(59)

 Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?

وَتَضْحَكُونَ وَلَا تَبْكُونَ(60)

 Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?

وَأَنتُمْ سَامِدُونَ(61)

 Alhãli kunã mãsu wãsã?

فَاسْجُدُوا لِلَّهِ وَاعْبُدُوا ۩(62)

 To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).


More surahs in Hausa:


Al-Baqarah Al-'Imran An-Nisa'
Al-Ma'idah Yusuf Ibrahim
Al-Hijr Al-Kahf Maryam
Al-Hajj Al-Qasas Al-'Ankabut
As-Sajdah Ya Sin Ad-Dukhan
Al-Fath Al-Hujurat Qaf
An-Najm Ar-Rahman Al-Waqi'ah
Al-Hashr Al-Mulk Al-Haqqah
Al-Inshiqaq Al-A'la Al-Ghashiyah

Download surah An-Najm with the voice of the most famous Quran reciters :

surah An-Najm mp3 : choose the reciter to listen and download the chapter An-Najm Complete with high quality
surah An-Najm Ahmed El Agamy
Ahmed Al Ajmy
surah An-Najm Bandar Balila
Bandar Balila
surah An-Najm Khalid Al Jalil
Khalid Al Jalil
surah An-Najm Saad Al Ghamdi
Saad Al Ghamdi
surah An-Najm Saud Al Shuraim
Saud Al Shuraim
surah An-Najm Abdul Basit Abdul Samad
Abdul Basit
surah An-Najm Abdul Rashid Sufi
Abdul Rashid Sufi
surah An-Najm Abdullah Basfar
Abdullah Basfar
surah An-Najm Abdullah Awwad Al Juhani
Abdullah Al Juhani
surah An-Najm Fares Abbad
Fares Abbad
surah An-Najm Maher Al Muaiqly
Maher Al Muaiqly
surah An-Najm Muhammad Siddiq Al Minshawi
Al Minshawi
surah An-Najm Al Hosary
Al Hosary
surah An-Najm Al-afasi
Mishari Al-afasi
surah An-Najm Yasser Al Dosari
Yasser Al Dosari


Saturday, May 4, 2024

لا تنسنا من دعوة صالحة بظهر الغيب