Surah Ash-Shu'ara
PDF —
Built right in your browser — download starts automatically
Surah Ash-Shu'ara pdf — Sauke (Hausa)
Surah Ash-Shu'ara pdf Hausa — Sauke Surah Ash-Shu'ara Fassara. Ash-Shu'ara (Meccan) 227 Aya.
Related
- Ash-Shu'ara FassaraHausa
- Ash-Shu'ara mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah Ash-Shu'ara

ﭑﭒ
¦. S̃. M̃.
ﭓﭔﭕﭖﭗ
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞ
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
ﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪ
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
ﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴﭵﭶ
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
ﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋ
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
ﮖﮗﮘﮙﮚﮛ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤ
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
ﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
ﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
ﯵﯶﯷﯸﯹﯺ
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."
ﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅ
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
ﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍ
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗ
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
ﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽ
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
ﭾﭿﮀﮁﮂﮃ
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
ﮄﮅﮆﮇﮈﮉ
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
ﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥ
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
ﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
ﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
ﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪ
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
ﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳ
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"
ﯴﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻ
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
ﯼﯽﯾﯿﰀ
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
ﰁﰂﰃﰄﰅﰆ
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
ﰇﰈﰉﰊﰋﰌ
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘ
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
ﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥ
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
ﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
ﮈﮉﮊﮋ
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
ﮌﮍﮎﮏﮐ
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
ﮑﮒﮓﮔ
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
ﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
ﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.
ﯭﯮﯯﯰﯱﯲ
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
ﯳﯴﯵﯶﯷ
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
ﯸﯹﯺﯻ
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
ﯼﯽﯾﯿ
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
ﰀﰁﰂﰃﰄ
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.
ﰅﰆﰇﰈ
Da taskõki da mazauni mai kyau.
ﰉﰊﰋﰌﰍﰎ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
ﰏﰐﰑ
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙ
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
ﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡ
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
ﭢﭣﭤﭥﭦﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
ﭱﭲﭳﭴ
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
ﭻﭼﭽﭾ
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
ﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
ﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
ﮏﮐﮑﮒﮓ
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
ﮛﮜﮝﮞﮟﮠﮡ
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
ﮢﮣﮤﮥﮦﮧ
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
ﮨﮩﮪﮫﮬ
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
ﯕﯖﯗﯘﯙﯚ
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
ﯛﯜﯝﯞ
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥ
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
ﯦﯧﯨﯩﯪ
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
ﯫﯬﯭﯮﯯ
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
ﯰﯱﯲﯳﯴ
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
ﯵﯶﯷﯸﯹ
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂ
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
ﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗ
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤ
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
ﭥﭦﭧﭨﭩ
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷ
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
ﭸﭹﭺﭻ
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
ﭼﭽﭾﭿ
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅﮆ
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
ﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
ﮏﮐﮑﮒﮓ
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.
ﮔﮕﮖﮗ
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
ﮘﮙﮚﮛﮜ
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
ﮤﮥﮦﮧﮨ
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
ﮩﮪﮫﮬﮭ
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
ﮮﮯﮰﮱﯓ
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
ﯔﯕﯖﯗ
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
ﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟ
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
ﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
ﯰﯱﯲﯳﯴ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
ﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼ
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
ﯽﯾﯿﰀﰁ
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
ﰂﰃﰄﰅ
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
ﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍﰎﰏﰐﰑﰒ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
ﰓﰔﰕﰖ
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
ﰗﰘﰙﰚﰛﰜﰝ
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗ
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟﭠ
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."
ﭡﭢﭣﭤﭥ
"Ban zama mai kõre mũminai ba."
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫ
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
ﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄ
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋ
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
ﮌﮍﮎﮏﮐ
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
ﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
ﮡﮢﮣﮤ
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
ﮭﮮﮯﮰﮱ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
ﯓﯔﯕﯖ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
ﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣ
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
ﯪﯫﯬﯭﯮ
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"
ﯯﯰﯱﯲﯳ
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
ﯴﯵﯶﯷ
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
ﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
ﯾﯿﰀﰁ
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
ﰂﰃﰄ
"Da gõnaki da marẽmari."
ﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋ
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
ﰌﰍﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕ
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."
ﭗﭘﭙﭚ
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
ﭛﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦﭧ
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
ﭨﭩﭪﭫﭬﭭ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
ﭮﭯﭰﭱ
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
ﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹ
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
ﭺﭻﭼﭽﭾ
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
ﭿﮀﮁﮂ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎﮏ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
ﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
ﮖﮗﮘﮙ
"A cikin gõnaki da marẽmari."
ﮚﮛﮜﮝﮞ
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"
ﮟﮠﮡﮢﮣﮤ
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
ﮥﮦﮧﮨ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
ﮩﮪﮫﮬﮭ
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕ
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
ﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧ
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
ﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱ
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
ﯲﯳﯴﯵﯶﯷﯸﯹ
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
ﯺﯻﯼﯽ
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
ﯾﯿﰀﰁﰂﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊ
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
ﰋﰌﰍﰎﰏﰐ
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
ﭑﭒﭓﭔﭕ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
ﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
ﭞﭟﭠﭡﭢ
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
ﭣﭤﭥﭦ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
ﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
ﭴﭵﭶﭷﭸ
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃﮄﮅ
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"
ﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
ﮛﮜﮝﮞ
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
ﮟﮠﮡﮢﮣ
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
ﮤﮥﮦﮧ
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.
ﮨﮩﮪﮫﮬﮭﮮﮯ
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
ﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘﯙﯚ
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
ﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
ﯡﯢﯣﯤﯥ
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
ﯭﯮﯯﯰﯱ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
ﯲﯳﯴﯵ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
ﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂ
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
ﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊ
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
ﰋﰌﰍﰎ
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
ﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕﰖﰗﰘ
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
ﭗﭘﭙﭚﭛﭜ
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
ﭝﭞﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
ﭧﭨﭩﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶ
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
ﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂ
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋﮌ
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
ﮍﮎﮏﮐﮑﮒ
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
ﮓﮔﮕﮖﮗ
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
ﮘﮙﮚﮛﮜ
Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
ﮣﮤﮥﮦ
Da harshe na Larabci mai bayãni.
ﮧﮨﮩﮪﮫ
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
ﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?
ﯗﯘﯙﯚﯛﯜ
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
ﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣ
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱ
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
ﯲﯳﯴﯵﯶﯷ
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
ﯸﯹﯺﯻﯼ
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
ﯽﯾﯿ
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
ﰀﰁﰂﰃﰄ
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
ﰅﰆﰇﰈﰉﰊ
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗ
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞﭟ
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
ﭠﭡﭢﭣﭤ
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
ﭥﭦﭧﭨﭩ
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
ﭰﭱﭲﭳﭴ
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
ﭿﮀﮁﮂ
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉ
Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
ﮒﮓﮔﮕﮖ
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
ﮗﮘﮙﮚﮛ
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
ﮜﮝﮞﮟ
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
ﮠﮡﮢﮣﮤ
Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani.
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
ﮬﮭﮮﮯﮰﮱ
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
ﯓﯔﯕﯖﯗ
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
ﯘﯙﯚﯛ
Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡﯢﯣ
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱﯲﯳﯴﯵﯶﯷﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾ
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.
Al-Kur'ani
Tuesday, August 18, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







