Wallazeena tabawwa`ud daara wal eemaana min qablihim yuhibboona man haajara ilaihim wa laa yajidoona fee sudoorihim haajatam mimmaa ootoo wa yu`siroona `alaa anfusihim wa law kaana bihim khasaasah; wa many yooqa shuhha nafsihee fa ulaaa`ika humul muflihoon
📖 Fassara (Da Hausa)
📖 Da Hausa
Da waɗanda suka zaunar da gidãjensu (ga Musulunci) kuma (suka zãɓi) ĩmãni, a gabãnin zuwansu, sunã son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma bã su tunãnin wata bukãta a cikin ƙirãzansu daga abin da aka bai wa muhãjirĩna, kuma sunã fĩfĩta waɗansu a kan kãwunansu, kuma ko dã sunã da wata larũra. Wanda ya sãɓã wa rõwar ransa, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
"تَبَوَّءُوا الدَّارَ": Sun zauna a Madina, wato Ansar (mazaunan Madina) waɗanda suka zauna a gidan hijira.
"وَالإِيمَانَ": Sun haɗa zama a Madina da kuma tsayawa a kan imani da ƙarfi.
"حَاجَةً": A nan ana nufin ƙishi ko haushi ko ɓacin rai.
"خَصَاصَةٌ": Talauci ko buƙata ko ƙarancin abin duniya.
"شُحَّ نَفْسِهِ": Rowa ko yunwar zuciya ga dukiya, da kuma tsananin son tara ta da kuma rufewa.
Fassarar Ayar:
Ayar tana magana ne game da Ansar (mazaunan Madina) waɗanda suka zauna a gidan hijira (Madina) kuma suka tabbatar da imani kafin zuwan Manzon Allah (SAW) da kuma Muhajirun daga Makka. Waɗannan Ansar suna ƙaunar waɗanda suka yi hijira zuwa gare su, kuma ba su samu a cikin zukatansu wani ƙishi ko haushi ba game da abin da aka ba wa Muhajirun daga dukiyar da aka samu (kamar dukiyar Banu Nadir), ko da yake ba a ba su ba.
Sun fifita Muhajirun a kan kansu a cikin abubuwan duniya, har ma da lokacin da su kansu ke cikin talauci da buƙata. Suna ba da abin da suke da shi ga 'yan'uwansu Muhajirun, suna raba musu gidajensu da dukiyoyinsu, suna nuna kyautatawa da karimci mafi girma.
A ƙarshen ayar, Allah ya bayyana cewa duk wanda Allah ya tsare shi daga rowar zuciyarsa (wato yunwar dukiya da son tara ta ba tare da biyan haƙƙin Allah ba), to waɗannan su ne masu cin nasara a duniya da lahir
Da waɗanda suka zaunar da gidãjensu (ga Musulunci) kuma (suka zãɓi) ĩmãni, a gabãnin zuwansu, sunã son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma bã su tunãnin wata bukãta a cikin ƙirãzansu daga abin da aka bai wa muhãjirĩna, kuma sunã fĩfĩta waɗansu a kan kãwunansu, kuma ko dã sunã da wata larũra. Wanda ya sãɓã wa rõwar ransa, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
Abin da Allah Ya sanya shi ganĩma ga ManzonSa dagamutãnen ƙauyukan nan, to, na Allah ne, kuma na ManzonSa ne kuma na mãsu dangantaka da mãrayu da miskĩnai da ɗan hanya (matafiyi) ne dõmin kada ya kasance abin shãwãgi a tsakãnin mawadãta daga cikinku kuma abin da Manzo ya bã ku, to, ku kama shi, kuma abin da ya hane ku, to, ku bar shi. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle, Allah, Mai tsananin uƙũba ne.
(Ku yi mãmãki) Ga matalauta mãsu hijira waɗanda aka fitar daga gidãjẽnsu da dũkiyõyinsu, sunã nẽman falala daga Allah da kuma yarda, kuma sunã taimakon Allah da ManzonSa! Waɗannan sũ ne mãsu gaskiya.
Da waɗanda suka zaunar da gidãjensu (ga Musulunci) kuma (suka zãɓi) ĩmãni, a gabãnin zuwansu, sunã son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma bã su tunãnin wata bukãta a cikin ƙirãzansu daga abin da aka bai wa muhãjirĩna, kuma sunã fĩfĩta waɗansu a kan kãwunansu, kuma ko dã sunã da wata larũra. Wanda ya sãɓã wa rõwar ransa, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
Kuma waɗanda suka zõ daga bãyansu, sunã cẽwa, "Yã Ubangijinmu! Ka yi gãfara a gare mu, kuma ga 'yan'uwanmu, waɗanda da suka riga mu yin ĩmãni, kada Ka sanya wani ƙulli a cikin zukãtanmu ga waɗanda suka yi ĩmãni. Yã Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jin ƙai.
Ashe, ba ka ga waɗanda suka yi munãfinci ba, sunã cẽwa ga 'yan'uwansu, waɗanda suka kãfirta daga Mazõwa Littafi, "Lalle idan an fitar da ku, lalle zã mu fita tãre da ku, kuma bã zã mu yi ɗã'a ga kõwa ba game da ku, har abada, kuma lalle idan an yãƙe ku, lalle zã mu taimake ku haƙĩƙatan?" Alhãli kuwa Allah na shaidar cẽwa lalle sũ tabbas, maƙaryata ne.
SurahQuran.com was founded as a humble effort to serve the Noble Book and the pure Sunnah, to invite people to Allah, and to make the religious sciences accessible according to the methodology of the Quran and Sunnah. We praise and thank Allah for His grace, and we ask Him to accept our work and make it sincere for His noble Face.