Qul halumma shuhadaaa`akumul lazeena yash hadoona annal laaha harrama haazaa fa in shahidoo falaa tashhad ma`ahum; wa laa tattabi` ahwaaa`al lazeena kazzaboo bi Aayaatinaa wallazeena laa yu`minoona bil Aakhirati wa hum bi Rabbihim ya`diloon
📖 Fassara (Da Hausa)
📖 Da Hausa
Ka ce: "Ku kãwo shaidunku, waɗanda suke bãyar da shaidar cẽwa Allah ne Ya haramta wannan." To idan sun kãwo shaida kada ka yi shaida tãre da su. Kuma kada ka bi son zũciyõyin waɗanda suka ƙaryata, game da ãyõyinMu, da waɗanda bã su yin ĩmãni da Lãhira, alhãli kuwa sũ daga Ubangijinsu suna karkacẽwa.
هَلُمَّ: Kalmar kira ce da ake nufin "ku zo" ko "ku kawo".
يَعْدِلُونَ: A nan yana nufin suna daidaita Allah da wasu (suna yin shirka).
Fassarar Ayar:
Ka ce, ya Muhammad, ga waɗannan mushrikai da suke haramta abin da Allah ya halatta, kuma suna da'awar cewa Allah ne ya haramta waɗannan abubuwa: "Ku kawo shaidunku waɗanda suke shaida cewa Allah ne ya haramta waɗannan abubuwan da kuka haramta." Idan suka zo da shaidu, to kada ka yarda da su, domin su shaidun ƙarya ne, ba su da wani ilmi a kan abin da suke faɗa. Kuma kada ka bi son zuciyar waɗanda suka ƙaryata ayoyinMu, waɗanda suka haramta abin da Allah ya halatta, suka halatta abin da Allah ya haramta, bisa son zuciyarsu kawai. Kuma kada ka bi waɗanda ba su yi imani da Lahira ba, waɗanda suke yin shirka da Ubangijinsu, suna daidaita masa wasu abubuwan bauta. To yaya za a bi mutumin da hali irin wannan yake da Ubangijinsa?
Fa'idodin Darasi:
Wannan ayar tana nuna cewa haramci da halacci suna bin nassin Allah ne kawai, ba bin son zuciyar mutane ko al'adunsu ba.
Tana karfafa gaskiya wajen ba da shaida, da kuma hana shaidar ƙarya, musamman idan aka danganta wani abu ga Allah da bai faɗa ba.
Tana gargadin manzon Allah (SAW) da al'ummarsa daga bin son zuciya, domin son zuciya na kaiwa ga ƙaryata ayoyin Allah da rashin imani da Lahira.
Tana nuna cewa shirka da daidaita Allah da wasu abubuwa daga cikin mafi girman dalilan da ke janyo ɓata tunani da aiki, saboda haka dole ne a nisanta daga shi.
Tana ƙarfafa miƙa kai ga hukuncin Allah kawai, ba ga hukunce-hukuncen da suka saba wa nassi ba, ko da kuwa waɗanda suke da'awar suna da masaniya.
Ka ce: "Ku kãwo shaidunku, waɗanda suke bãyar da shaidar cẽwa Allah ne Ya haramta wannan." To idan sun kãwo shaida kada ka yi shaida tãre da su. Kuma kada ka bi son zũciyõyin waɗanda suka ƙaryata, game da ãyõyinMu, da waɗanda bã su yin ĩmãni da Lãhira, alhãli kuwa sũ daga Ubangijinsu suna karkacẽwa.
Waɗanda suka yi shirki zã su ce: "Dã Allah Yã so dã ba mu yi shirki ba, kuma dã ubanninmu ba su yi ba, kuma dã ba mu haramta wani abu ba." Kamar wannan ne mutãnen da suke a gabãninsu suka ƙaryata, har suka ɗanɗani azãbarMu. Ka ce: "Shin, kunã da wani ilmi a wurinku dõmin ku fito mana da shi? Bã ku bin kõme fãce zato kuma ba ku zama ba fãce ƙiri-faɗi kawai kuke yi."
Ka ce: "Ku kãwo shaidunku, waɗanda suke bãyar da shaidar cẽwa Allah ne Ya haramta wannan." To idan sun kãwo shaida kada ka yi shaida tãre da su. Kuma kada ka bi son zũciyõyin waɗanda suka ƙaryata, game da ãyõyinMu, da waɗanda bã su yin ĩmãni da Lãhira, alhãli kuwa sũ daga Ubangijinsu suna karkacẽwa.
Ka ce: "Ku zo, in karanta abin da Ubangijinku Ya haramta." wãjibi ne a kanku kada ku yi shirkin kõme da Shi, kuma ga mahaifa biyu (ku kyautata) kyautatãwa, kuma kada ku kashe ɗiyanku sabõda talauci, Mũ ne Muke azurta ku, kũ da su, kuma kada ku kusanci abũbuwa alfãsha, abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya ɓõyu, kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta, fãce da hakki. Wannan ne (Allah) Ya yi muku wasiyya da Shi: Tsammãninku, kunã hankalta.
Kada ku kusanci dũkiyar marãya fãce da wadda take ita ce mafi kyau, har ya kai ga ƙarfinsa. Kuma ku cika mũdu da sikẽli da ãdalci, bã Mu kallafã wa rai fãce iyãwarsa. Kuma idan kun faɗi magana, to, ku yi ãdalci, kuma ko dã yã kasance ma'abũcin zumunta ne. Kuma da alkawarin Allah ku cika. wannan ne Ya yi muku wasiyya da shi: Tsammãninku, kunã tunãwa.
SurahQuran.com was founded as a humble effort to serve the Noble Book and the pure Sunnah, to invite people to Allah, and to make the religious sciences accessible according to the methodology of the Quran and Sunnah. We praise and thank Allah for His grace, and we ask Him to accept our work and make it sincere for His noble Face.