Wa man azlamu mimmanif taraa `alal laahi kaziban aw qaala oohiya ilaiya wa lam yooha ilaihi shai`un wa man qaala sa unzilu misla maaa anzalal laah; wa law taraaa iziz zaalimoona fee ghamaraatil mawti walmalaaa`ikatu baasitooo aideehim akhrijooo anfusakum; al yawma tujzawna `azaabal hooni bimaa kuntum taqooloona `alal laahi ghairal haqqi wa kuntum `an aayaatihee tastakbiroon
📖 Fassara (Da Hausa)
📖 Da Hausa
Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ce: "An yi wahayi zuwa gare ni," alhãli kuwa ba a yi wahayin kõme ba zuwa gare shi, da wanda ya ce: "zan saukar da misãlin abin da Allah Ya saukar?" Kuma dã kã gani, a lõkacin da azzãlumai suke cikin mãyen mutuwa, kuma malã'iku sunã mãsu shimfiɗa hannuwansu, (sunã ce musu) "Ku fitar da kanku; a yau anã sãka muku da azãbar wulãƙanci sabõda abin da kuka kasance kunã faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma kun kasance daga ãyõyinSa kunã yin girman kai."
Ghamaratil mawt: Tsananin wahalar mutuwa da ɓacin rai.
Basitu aydihim: Mala'iku suna miƙa hannuwansu don ɗaukar rayukan.
Azabal hoon: Azaba mai wulakantarwa da ƙasƙantarwa.
Tastakbirun: Kuna girman kai da ƙin biyayya.
Fassarar Ayar:
Babu wanda ya fi zalunci ga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kamar wanda ya ce: "Allah bai saukar da wani abu ba ga wani mutum ba," ko kuma wanda ya yi ƙarya ya ce: "An yi wahayi zuwa gare ni," alhali ba a yi masa wahayin kome ba. Haka kuma wanda ya ce: "Zan saukar da irin abin da Allah ya saukar na Alƙur'ani." Wannan magana ta fito daga waɗanda suka yi izgili da Alƙur'ani, kamar Musailima maƙaryaci da abokanansa.
Idan kai (ya Muhammad) da ka ga yanayin waɗannan azzalumai a lokacin da suke cikin tsananin wahalar mutuwa, da Mala'iku suna miƙa hannuwansu don ɗaukar rayukansu da azabtar da su, suna ce musu: "Ku fitar da rayukanku! A yau za a saka muku da azaba mai wulakantarwa, saboda abin da kuka kasance kuna faɗi na ƙarya a kan Allah, da kuma girman kai da kuke yi ga ayoyinSa, ba ku yarda da su ba." Da ka ga wannan, da ka ga abin al'ajabi mai girma.
Fa'idodin Ayar:
Babban zalunci shi ne ƙirƙira ƙarya a kan Allah, kamar da'awar annabci ko samun wahayi ba tare da gaskiya ba.
Waɗanda suke ƙoƙarin kwatanta Alƙur'ani ko su ce za su iya kawo irinsa, suna cikin manyan azzalumai, domin Alƙur'ani kalmar Allah ce da ba za a iya kwatanta ta ba.
Mutuwa tana da tsananin wahala ga azzalumai, kuma Mala'iku suna azabtar da su a lokacin ɗaukar rayukansu.
Sakamakon ƙarya da girman kai ga ayoyin Allah shine wulakanci a duniya da la'ana a lahira.
Ayat tana gargadinmu mu nisanci ƙarya da girman kai, mu kuma yi imani da Alƙur'ani da annabcin Muhammad (SAW) da kyakkyawar ɗabi'a.
Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ce: "An yi wahayi zuwa gare ni," alhãli kuwa ba a yi wahayin kõme ba zuwa gare shi, da wanda ya ce: "zan saukar da misãlin abin da Allah Ya saukar?" Kuma dã kã gani, a lõkacin da azzãlumai suke cikin mãyen mutuwa, kuma malã'iku sunã mãsu shimfiɗa hannuwansu, (sunã ce musu) "Ku fitar da kanku; a yau anã sãka muku da azãbar wulãƙanci sabõda abin da kuka kasance kunã faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma kun kasance daga ãyõyinSa kunã yin girman kai."
Kuma ba su ƙaddara Allah a kan hakkin ƙaddara shi ba, a lõkacin da suka ce: "Allah bai saukar da kõme ba ga wani mutum." Ka ce: "Wãne ne ya saukar da Littãfi wanda Mũsã ya zo da shi, yanã haske da shiriya ga mutãne, kunã sanya shi takardu, kũna bayyana su, kuma kunã ɓõye mai yawa, kuma an sanar da ku abin da ba ku sani ba, ku da ubanninku?" Ka ce: "Allah," sa'an nan ka bar su a cikin sharhõliyarsu sunã wãsã.
Kuma wannan Littãfi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, mai gaskata wanda yake a gabansa ne, kuma dõmin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu (Makka) da wanda yake gefenta. Kuma waɗanda suke yin ĩmãni da Lãhira sunã ĩmãni da shi (Alƙur'ãni), kuma sũ, a kan sallarsu, sunã tsarẽwa.
Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ce: "An yi wahayi zuwa gare ni," alhãli kuwa ba a yi wahayin kõme ba zuwa gare shi, da wanda ya ce: "zan saukar da misãlin abin da Allah Ya saukar?" Kuma dã kã gani, a lõkacin da azzãlumai suke cikin mãyen mutuwa, kuma malã'iku sunã mãsu shimfiɗa hannuwansu, (sunã ce musu) "Ku fitar da kanku; a yau anã sãka muku da azãbar wulãƙanci sabõda abin da kuka kasance kunã faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma kun kasance daga ãyõyinSa kunã yin girman kai."
Kuma lalle ne haƙĩƙa, kun zo Mana ɗai ɗai, kamar yadda Muka halittã ku a farkon lõkaci. Kuma kun bar abin da Muka mallaka muku a bayan bayayyakinku, kuma ba Mu gani a tãre da kũ ba, macẽtanku waɗanda kuka riya cẽwa lalle ne sũ, a cikinku mãsu tãrayya ne. Lalle ne, hãƙĩƙa, kõme yã yanyanke a tsakãninku, kuma abin da kuka kasance kunã riyãwa ya ɓace daga gare ku.
Lalle ne, Allah ne Mai tsãgewar ƙwãyar hatsi da kwalfar gurtsu. Yanã fitar da mai rai daga mamaci, kuma (Shi) Mai fitar da mamaci ne daga mai rai, wannan ne Allah. To, yãya ake karkatar da ku?
SurahQuran.com was founded as a humble effort to serve the Noble Book and the pure Sunnah, to invite people to Allah, and to make the religious sciences accessible according to the methodology of the Quran and Sunnah. We praise and thank Allah for His grace, and we ask Him to accept our work and make it sincere for His noble Face.