Surah Adh-Dhariyat pdf — Sauke (Hausa)
Surah Adh-Dhariyat pdf Hausa — Sauke Surah Adh-Dhariyat Fassara. Surah Adh-Dhariyat (Meccan) 60 Aya.
Related
- Surah Adh-Dhariyat FassaraHausa
- Surah Adh-Dhariyat mp3Saurara
- Quran Index Hausa114
More Surah PDF
Surah Adh-Dhariyat

ﯤﯥﯦ
51:1
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
ﯧﯨﯩ
51:2
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
ﯪﯫﯬ
51:3
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
ﯭﯮﯯ
51:4
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
ﯰﯱﯲﯳ
51:5
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
ﯴﯵﯶﯷ
51:6
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
ﭑﭒﭓﭔ
51:7
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
ﭕﭖﭗﭘﭙ
51:8
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
ﭚﭛﭜﭝﭞ
51:9
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
ﭟﭠﭡ
51:10
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
ﭢﭣﭤﭥﭦﭧ
51:11
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
ﭨﭩﭪﭫﭬ
51:12
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
51:13
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
51:14
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
51:15
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
ﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋ
51:16
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒ
51:17
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
ﮓﮔﮕﮖ
51:18
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
51:19
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
ﮝﮞﮟﮠﮡ
51:20
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
ﮢﮣﮤﮥﮦﮧ
51:21
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
ﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
51:22
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔﯕﯖﯗﯘ
51:23
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
ﯙﯚﯛﯜﯝﯞﯟ
51:24
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
ﯠﯡﯢﯣﯤﯥﯦﯧﯨﯩﯪ
51:25
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
ﯫﯬﯭﯮﯯﯰﯱ
51:26
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
ﯲﯳﯴﯵﯶﯷ
51:27
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
ﯸﯹﯺﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂﰃ
51:28
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
ﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌﰍ
51:29
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
ﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕﰖﰗ
51:30
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗ
51:31
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞ
51:32
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
ﭟﭠﭡﭢﭣﭤ
51:33
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
ﭥﭦﭧﭨﭩ
51:34
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯﭰ
51:35
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
51:36
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
51:37
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
ﮁﮂﮃﮄﮅﮆﮇﮈﮉ
51:38
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏﮐ
51:39
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖﮗﮘ
51:40
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
ﮙﮚﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
51:41
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
51:42
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
51:43
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
ﯕﯖﯗﯘﯙﯚﯛﯜﯝ
51:44
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
ﯞﯟﯠﯡﯢﯣﯤﯥ
51:45
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫﯬﯭﯮﯯ
51:46
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
ﯰﯱﯲﯳﯴﯵ
51:47
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
ﯶﯷﯸﯹﯺ
51:48
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
ﯻﯼﯽﯾﯿﰀﰁﰂ
51:49
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
ﰃﰄﰅﰆﰇﰈﰉﰊﰋﰌ
51:50
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
ﰍﰎﰏﰐﰑﰒﰓﰔﰕﰖﰗﰘﰙ
51:51
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖﭗﭘﭙﭚﭛﭜﭝﭞ
51:52
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
ﭟﭠﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
51:53
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
ﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
51:54
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲ
51:55
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸﭹ
51:56
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿﮀﮁﮂﮃ
51:57
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
ﮄﮅﮆﮇﮈﮉﮊﮋ
51:58
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
51:59
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
ﮖﮗﮘﮙﮚﮛﮜﮝ
51:60
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
Al-Kur'ani
Wednesday, September 9, 2026
Don't forget us in your sincere prayers







