19 Aya · Meccan · Hausa
bismillah
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
ﮛﮜﮝﮞﮟ
Ya hahitta mutum daga gudan jini.
ﮠﮡﮢﮣ
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
ﮤﮥﮦﮧ
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
ﮨﮩﮪﮫﮬﮭ
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
ﮮﮯﮰﮱﯓ
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
ﯔﯕﯖﯗ
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
ﯘﯙﯚﯛﯜ
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
ﯝﯞﯟﯠ
Shin, kã ga wanda ke hana.
ﯡﯢﯣﯤ
Bãwã idan yã yi salla?
ﯥﯦﯧﯨﯩﯪ
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
ﯫﯬﯭﯮ
Ko ya yi umurni da taƙawa?
ﭑﭒﭓﭔﭕ
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
ﭖﭗﭘﭙﭚﭛ
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡﭢ
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
ﭣﭤﭥﭦ
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
ﭧﭨﭩ
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
ﭪﭫﭬ
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).
ﭭﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).

Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers