سوره قلم به زبان هَوُسَ

  1. گوش دادن به سوره
  2. سورهای دیگر
  3. ترجمه سوره
قرآن کریم | ترجمه معانی قرآن | زبان هَوُسَ | سوره قلم | القلم - تعداد آیات آن 52 - شماره سوره در مصحف: 68 - معنی سوره به انگلیسی: The Pen.

ن ۚ وَالْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ(1)

 Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.

مَا أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍ(2)

 Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.

وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍ(3)

 Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ(4)

 Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.

فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ(5)

 Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.

بِأَييِّكُمُ الْمَفْتُونُ(6)

 Ga wanenku haukã take.

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِالْمُهْتَدِينَ(7)

 Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.

فَلَا تُطِعِ الْمُكَذِّبِينَ(8)

 Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.

وَدُّوا لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ(9)

 Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.

وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ(10)

 Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

هَمَّازٍ مَّشَّاءٍ بِنَمِيمٍ(11)

 Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.

مَّنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ(12)

 Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.

عُتُلٍّ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ(13)

 Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ(14)

 Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ(15)

 Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."

سَنَسِمُهُ عَلَى الْخُرْطُومِ(16)

 Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.

إِنَّا بَلَوْنَاهُمْ كَمَا بَلَوْنَا أَصْحَابَ الْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ(17)

 Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.

وَلَا يَسْتَثْنُونَ(18)

 Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.

فَطَافَ عَلَيْهَا طَائِفٌ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَائِمُونَ(19)

 Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.

فَأَصْبَحَتْ كَالصَّرِيمِ(20)

 Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

فَتَنَادَوْا مُصْبِحِينَ(21)

 Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

أَنِ اغْدُوا عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَارِمِينَ(22)

 Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.

فَانطَلَقُوا وَهُمْ يَتَخَافَتُونَ(23)

 Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).

أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا الْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌ(24)

 "Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"

وَغَدَوْا عَلَىٰ حَرْدٍ قَادِرِينَ(25)

 Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.

فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوا إِنَّا لَضَالُّونَ(26)

 Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ(27)

 "Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."

قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ(28)

 Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"

قَالُوا سُبْحَانَ رَبِّنَا إِنَّا كُنَّا ظَالِمِينَ(29)

 Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَلَاوَمُونَ(30)

 Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.

قَالُوا يَا وَيْلَنَا إِنَّا كُنَّا طَاغِينَ(31)

 Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

عَسَىٰ رَبُّنَا أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًا مِّنْهَا إِنَّا إِلَىٰ رَبِّنَا رَاغِبُونَ(32)

 "Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."

كَذَٰلِكَ الْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ الْآخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا يَعْلَمُونَ(33)

 Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّاتِ النَّعِيمِ(34)

 Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.

أَفَنَجْعَلُ الْمُسْلِمِينَ كَالْمُجْرِمِينَ(35)

 Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?

مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ(36)

 Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?

أَمْ لَكُمْ كِتَابٌ فِيهِ تَدْرُسُونَ(37)

 Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ(38)

 Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?

أَمْ لَكُمْ أَيْمَانٌ عَلَيْنَا بَالِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ الْقِيَامَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ(39)

 Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?

سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ(40)

 Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?

أَمْ لَهُمْ شُرَكَاءُ فَلْيَأْتُوا بِشُرَكَائِهِمْ إِن كَانُوا صَادِقِينَ(41)

 Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍ وَيُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ(42)

 Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.

خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۖ وَقَدْ كَانُوا يُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ وَهُمْ سَالِمُونَ(43)

 Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).

فَذَرْنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا الْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ(44)

 Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.

وَأُمْلِي لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِي مَتِينٌ(45)

 Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.

أَمْ تَسْأَلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَ(46)

 Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?

أَمْ عِندَهُمُ الْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ(47)

 Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

فَاصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ الْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌ(48)

 Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

لَّوْلَا أَن تَدَارَكَهُ نِعْمَةٌ مِّن رَّبِّهِ لَنُبِذَ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ مَذْمُومٌ(49)

 Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.

فَاجْتَبَاهُ رَبُّهُ فَجَعَلَهُ مِنَ الصَّالِحِينَ(50)

 Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

وَإِن يَكَادُ الَّذِينَ كَفَرُوا لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَارِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا الذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُ لَمَجْنُونٌ(51)

 Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"

وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ(52)

 Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.


سورهای بیشتر به زبان هَوُسَ:

سوره البقره آل عمران سوره نساء
سوره مائده سوره يوسف سوره ابراهيم
سوره حجر سوره کهف سوره مریم
سوره حج سوره قصص سوره عنکبوت
سوره سجده سوره یس سوره دخان
سوره فتح سوره حجرات سوره ق
سوره نجم سوره رحمن سوره واقعه
سوره حشر سوره ملک سوره حاقه
سوره انشقاق سوره أعلى سوره غاشية

دانلود سوره قلم با صدای معروف‌ترین قراء:

انتخاب خواننده برای گوش دادن و دانلود کامل سوره قلم با کیفیت بالا.
سوره قلم را با صدای احمد العجمی
أحمد العجمي
سوره قلم را با صدای ابراهيم الاخضر
ابراهيم الاخضر
سوره قلم را با صدای بندر بليلة
بندر بليلة
سوره قلم را با صدای خالد الجليل
خالد الجليل
سوره قلم را با صدای حاتم فريد الواعر
حاتم فريد الواعر
سوره قلم را با صدای خليفة الطنيجي
خليفة الطنيجي
سوره قلم را با صدای سعد الغامدي
سعد الغامدي
سوره قلم را با صدای سعود الشريم
سعود الشريم
سوره قلم را با صدای الشاطري
الشاطري
سوره قلم را با صدای صلاح ابوخاطر
صلاح بوخاطر
سوره قلم را با صدای عبد الباسط عبد الصمد
عبد الباسط
سوره قلم را با صدای عبد الرحمن العوسي
عبدالرحمن العوسي
سوره قلم را با صدای عبد الرشيد صوفي
عبد الرشيد صوفي
سوره قلم را با صدای عبد العزيز الزهراني
عبدالعزيز الزهراني
سوره قلم را با صدای عبد الله بصفر
عبد الله بصفر
سوره قلم را با صدای عبد الله عواد الجهني
عبد الله الجهني
سوره قلم را با صدای علي الحذيفي
علي الحذيفي
سوره قلم را با صدای علي جابر
علي جابر
سوره قلم را با صدای غسان الشوربجي
غسان الشوربجي
سوره قلم را با صدای فارس عباد
فارس عباد
سوره قلم را با صدای ماهر المعيقلي
ماهر المعيقلي
سوره قلم را با صدای محمد أيوب
محمد أيوب
سوره قلم را با صدای محمد المحيسني
محمد المحيسني
سوره قلم را با صدای محمد جبريل
محمد جبريل
سوره قلم را با صدای محمد صديق المنشاوي
المنشاوي
سوره قلم را با صدای الحصري
الحصري
سوره قلم را با صدای العفاسي
مشاري العفاسي
سوره قلم را با صدای ناصر القطامي
ناصر القطامي
سوره قلم را با صدای وديع اليمني
وديع اليمني
سوره قلم را با صدای ياسر الدوسري
ياسر الدوسري


Sunday, May 12, 2024

به قرآن کریم چنگ بزنید