Surah Al-Haqqah with Hausa

  1. Surah mp3
  2. More
  3. Hausa
The Holy Quran | Quran translation | Language Hausa | Surah Al-Haqqah | الحاقة - Ayat Count 52 - The number of the surah in moshaf: 69 - The meaning of the surah in English: The Sure Reality.

الْحَاقَّةُ(1)

 Kiran gaskiya!

مَا الْحَاقَّةُ(2)

 Mẽne ne kiran gaskiya?

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحَاقَّةُ(3)

 Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌ بِالْقَارِعَةِ(4)

 Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا بِالطَّاغِيَةِ(5)

 To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ(6)

 Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَانِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ(7)

 (Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّن بَاقِيَةٍ(8)

 To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

وَجَاءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُ وَالْمُؤْتَفِكَاتُ بِالْخَاطِئَةِ(9)

 Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

فَعَصَوْا رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً(10)

 Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

إِنَّا لَمَّا طَغَى الْمَاءُ حَمَلْنَاكُمْ فِي الْجَارِيَةِ(11)

 Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَا أُذُنٌ وَاعِيَةٌ(12)

 Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

فَإِذَا نُفِخَ فِي الصُّورِ نَفْخَةٌ وَاحِدَةٌ(13)

 To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

وَحُمِلَتِ الْأَرْضُ وَالْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَاحِدَةً(14)

 Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ(15)

 A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

وَانشَقَّتِ السَّمَاءُ فَهِيَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ(16)

 Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

وَالْمَلَكُ عَلَىٰ أَرْجَائِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَانِيَةٌ(17)

 Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ(18)

 A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ فَيَقُولُ هَاؤُمُ اقْرَءُوا كِتَابِيَهْ(19)

 To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَاقٍ حِسَابِيَهْ(20)

 "Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ(21)

 Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ(22)

 A cikin Aljanna maɗaukakiya.

قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ(23)

 Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا أَسْلَفْتُمْ فِي الْأَيَّامِ الْخَالِيَةِ(24)

 (Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِشِمَالِهِ فَيَقُولُ يَا لَيْتَنِي لَمْ أُوتَ كِتَابِيَهْ(25)

 Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ(26)

 "Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

يَا لَيْتَهَا كَانَتِ الْقَاضِيَةَ(27)

 "In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

مَا أَغْنَىٰ عَنِّي مَالِيَهْ ۜ(28)

 "Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

هَلَكَ عَنِّي سُلْطَانِيَهْ(29)

 "Ĩkona ya ɓace mini!"

خُذُوهُ فَغُلُّوهُ(30)

 (Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

ثُمَّ الْجَحِيمَ صَلُّوهُ(31)

 "Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

ثُمَّ فِي سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَاسْلُكُوهُ(32)

 "Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

إِنَّهُ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِاللَّهِ الْعَظِيمِ(33)

 "Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ(34)

 "Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

فَلَيْسَ لَهُ الْيَوْمَ هَاهُنَا حَمِيمٌ(35)

 "Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ(36)

 "Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

لَّا يَأْكُلُهُ إِلَّا الْخَاطِئُونَ(37)

 "Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

فَلَا أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ(38)

 To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

وَمَا لَا تُبْصِرُونَ(39)

 Da abin da bã ku iya gani.

إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ(40)

 Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ(41)

 Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ(42)

 Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَ(43)

 Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ الْأَقَاوِيلِ(44)

 Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِالْيَمِينِ(45)

 Dã Mun kãma shi da dãma.

ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ الْوَتِينَ(46)

 sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَاجِزِينَ(47)

 Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

وَإِنَّهُ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ(48)

 Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ(49)

 Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

وَإِنَّهُ لَحَسْرَةٌ عَلَى الْكَافِرِينَ(50)

 Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

وَإِنَّهُ لَحَقُّ الْيَقِينِ(51)

 Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.

فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ(52)

 Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.


More surahs in Hausa:


Al-Baqarah Al-'Imran An-Nisa'
Al-Ma'idah Yusuf Ibrahim
Al-Hijr Al-Kahf Maryam
Al-Hajj Al-Qasas Al-'Ankabut
As-Sajdah Ya Sin Ad-Dukhan
Al-Fath Al-Hujurat Qaf
An-Najm Ar-Rahman Al-Waqi'ah
Al-Hashr Al-Mulk Al-Haqqah
Al-Inshiqaq Al-A'la Al-Ghashiyah

Download surah Al-Haqqah with the voice of the most famous Quran reciters :

surah Al-Haqqah mp3 : choose the reciter to listen and download the chapter Al-Haqqah Complete with high quality
surah Al-Haqqah Ahmed El Agamy
Ahmed Al Ajmy
surah Al-Haqqah Bandar Balila
Bandar Balila
surah Al-Haqqah Khalid Al Jalil
Khalid Al Jalil
surah Al-Haqqah Saad Al Ghamdi
Saad Al Ghamdi
surah Al-Haqqah Saud Al Shuraim
Saud Al Shuraim
surah Al-Haqqah Abdul Basit Abdul Samad
Abdul Basit
surah Al-Haqqah Abdul Rashid Sufi
Abdul Rashid Sufi
surah Al-Haqqah Abdullah Basfar
Abdullah Basfar
surah Al-Haqqah Abdullah Awwad Al Juhani
Abdullah Al Juhani
surah Al-Haqqah Fares Abbad
Fares Abbad
surah Al-Haqqah Maher Al Muaiqly
Maher Al Muaiqly
surah Al-Haqqah Muhammad Siddiq Al Minshawi
Al Minshawi
surah Al-Haqqah Al Hosary
Al Hosary
surah Al-Haqqah Al-afasi
Mishari Al-afasi
surah Al-Haqqah Yasser Al Dosari
Yasser Al Dosari


Saturday, May 4, 2024

لا تنسنا من دعوة صالحة بظهر الغيب