Ya ce: "Bã zan sake shi tãre da kũ ba, sai kun kawo mini alkawarinku baga Allah, haƙĩƙa, kunã dawo mini da shi, sai fa idan an kẽwaye ku." To, a, lõkacinda suka yi mãsa alkawari, ya ce: "Allah ne wakĩli a kan abin da muke faɗa."
Yuhāta bikum: Sai dai idan an kewaye ku (ku mutu duka ko ku ci kujiya).
Wakīl: Shaida kuma mai kula da abin da muka faɗa.
Tafsirin Aya:
Ya’akubu (A.S.) ya ce wa ‘ya’yansa: “Ba zan aiko shi (Bunjamin) tare da ku ba, sai kun ba ni alkawari mai ƙarfi da Allah, cewa lalle za ku dawo da shi gare ni, sai dai idan an kewaye ku duka (ku mutu ko ku rasa iko).” Sa’ad da suka ba shi alkawarin da suka yi rantsuwa da Allah a kai, sai Ya’akubu ya ce: “Allah ne Wakili a kan abin da muke faɗa,” wato Allah ne shaida a kan wannan alkawari, kuma shi ne mai kiyaye mu.
Fa’idodin Aya:
Nuna mahimmancin amana da cika alkawari, domin Ya’akubu (A.S.) bai amince da su ba sai da suka ba shi alkawari mai ƙarfi da Allah.
Ilimin tarbiyyar ‘ya’ya: a yi taka tsantsan a kan al’amurra masu muhimmanci, kuma a nemi tabbaci daga mutum kafin a ba shi wani abu mai daraja.
Dogaro ga Allah a cikin dukkan al’amura, domin Ya’akubu (A.S.) bayan ya ɗauki alkawari ya mayar da al’amarin ga Allah, yana nuna cewa dukkan aiki ya dogara ga nufin Allah.
A cikin wannan aya akwai misali na yadda musulmi ya kamata ya kasance mai tsananin kiyaye amana da alkawari, kuma ya sa ido ga Allah a cikin dukkan ayyukansa.
Ya ce: "Bã zan sake shi tãre da kũ ba, sai kun kawo mini alkawarinku baga Allah, haƙĩƙa, kunã dawo mini da shi, sai fa idan an kẽwaye ku." To, a, lõkacinda suka yi mãsa alkawari, ya ce: "Allah ne wakĩli a kan abin da muke faɗa."
Ya ce: "Ashe, zã ni amince muku a kansa? Fãce dai kamar yadda na amince muku a kan ɗan'uwansa daga gabãni, sai dai Allah ne Mafĩfĩcin mãsu tsari, kuma Shĩ ne Mafi rahamar mãsu rahama."
Kuma a lõkacin da suka bũɗe kãyansu, suka sãmi hajjarsu an mayar musu da ita, suka ce: "Yã bãbanmu! Ba mu zãlunci! Wannan hajjarmu ce an mayar mana da ita, kuma mu nẽmo wa iyalinmu abinci, kuma mu kiyãye ɗan'uwanmu, kuma mu ƙãra awon kãyan rãƙumi guda, wancan awo ne mai sauki."
Ya ce: "Bã zan sake shi tãre da kũ ba, sai kun kawo mini alkawarinku baga Allah, haƙĩƙa, kunã dawo mini da shi, sai fa idan an kẽwaye ku." To, a, lõkacinda suka yi mãsa alkawari, ya ce: "Allah ne wakĩli a kan abin da muke faɗa."
Kuma ya ce: "Yã ɗiyana! Kada ku shiga ta ƙõfa guda, ku shiga ta ƙõfõfi dabam-dabam, kuma bã na wadãtar muku kõme daga Allah. Bãbu hukunci fãce daga Allah, a gare Shi na dõgara, kuma a gare Shi mãsu dõgara sai su dõgara."
Kuma a lõkacin da suka shiga daga inda ubansu ya umurce su wani abu bai kasance yanã wadãtarwa ga barinsu daga Allah ba fãce wata bukata ce a ran Yãƙũbu, ya bayyana ta. Kuma lalle ne shĩ, haƙĩƙa, ma'abũcin wani ilmi ne ga abin da Muka sanar da shi, kuma mafi yawan mutãne ba su sani ba.
Surah Yusuf Aya 66 - Karatu, Saurara, Fassara, Hausa : Ya ce: "Bã zan sake shi tãre da kũ ba,…
Surah Aya 66/111 — Surah Yusuf يوسف (Meccan). Karatu Saurara Fassara (Hausa). Saurara: Surah Yusuf Saurara, Surah Yusuf Fassara, Surah Yusuf mp3, Surah Yusuf pdf. Aya 64–68. Da Hausa: العربية.
SurahQuran.com was founded as a humble effort to serve the Noble Book and the pure Sunnah, to invite people to Allah, and to make the religious sciences accessible according to the methodology of the Quran and Sunnah. We praise and thank Allah for His grace, and we ask Him to accept our work and make it sincere for His noble Face.