An-Nisa · 21/176
Fassara Rubutun sauti — Surah An-Nisa
وَكَيْفَ تَأْخُذُونَهُ وَقَدْ أَفْضَىٰ بَعْضُكُمْ إِلَىٰ بَعْضٍ وَأَخَذْنَ مِنكُم مِّيثَاقًا غَلِيظًا ۝٢١
Wa kaifa taakhuzoonahoo wa qad afdaa ba`dukum ilaa ba`dinw wa akhazna minkum meesaaqan ghaleezaa
📖 Da Hausa
Kuma yãyã zã ku karɓe shi alhãli kuwa, haƙĩƙa, sãshenkuyã sãdu zuwa ga sãshe, kuma sun riƙi alkawari mai kauri daga gare ku?

🎧 Saurara
📜

Fassara — Tafsir

Ma'anar Kalmomi:

  • أَفْضَىٰ بَعْضُكُمْ إِلَىٰ بَعْضٍ: Sanya juna a ɓoye, wato saduwar aure (jima'i) tsakanin miji da mata.
  • مِيثَاقًا غَلِيظًا: Alkawari mai ƙarfi da tsanani, wato alkawarin aure da aka ɗauka da sunan Allah.

Tafsirin Ayar:

Yaya kuke iya karɓar abin da kuka bayar na sadaki (mahr) daga matan ku, alhali kuwa kun riga kun shiga juna ta hanyar saduwar aure, kuma kun ɗanɗana jin daɗin juna da soyayya da kuma buɗe wa juna asirai? Bayan wannan dangantaka ta kusanci, komawar karɓar sadaki zai zama abin ƙyama da rashin mutunci. Kuma kuwa matan sun ɗauki alkawari mai ƙarfi daga gare ku, wato alkawarin aure wanda aka kulla da sunan Allah da kuma bin shari'arsa, wanda ya wajabta ku riƙe su da kyautatawa ko ku sake su da kyautatawa. Don haka, karɓar abin da kuka bayar na sadaki bayan wannan alkawari babban zalunci ne da rashin bin Allah.

Fa'idodin Darasi:

  1. Nuna girman darajar aure da tsarkinsa, domin Allah ya sanya shi alkawari mai ƙarfi da ya kamata a mutunta.
  2. Ƙarfafa kyakkyawar dangantaka tsakanin ma'aurata, domin saduwa da kusanci suna ƙara haɗa zuciyoyi da nuna amana.
  3. Hana cin zarafin mata da ƙwace musu dukiyoyinsu, wanda ke nuna cewa Musulunci yana kare haƙƙin mata sosai.
  4. Tunatar da maza cewa su riƙe matansu da kyautatawa ko su sake su da kyautatawa, ba tare da cutar da su ba, wanda ke ƙarfafa zaman lafiya a cikin iyali.
  5. Nuna cewa Musulunci yana koyar da ɗabi'a mai kyau da mutunta alƙawura, waɗanda suke daga tushen imani.


📜 Aya 19-23 — Surah An-Nisa

19يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا لَا يَحِلُّ لَكُمْ أَن تَرِثُوا النِّسَاءَ كَرْهًا ۖ وَلَا تَعْضُلُوهُنَّ لِتَذْهَبُوا بِبَعْضِ مَا آتَيْتُمُوهُنَّ إِلَّا أَن يَأْتِينَ بِفَاحِشَةٍ مُّبَيِّنَةٍ ۚ وَعَاشِرُوهُنَّ بِالْمَعْرُوفِ ۚ فَإِن كَرِهْتُمُوهُنَّ فَعَسَىٰ أَن تَكْرَهُوا شَيْئًا وَيَجْعَلَ اللَّهُ فِيهِ خَيْرًا كَثِيرًا
Ku waɗanda suka yi ĩmãni! Bã ya halatta a gare ku, ku gãji mãtã a kan tĩlas kuma kadaku hana su aure dõmin ku tafi da sãshen abin da kuka ba su, fãce idan suka zo da wata alfãsha bayya nanniya kuma ku yi zamantakẽwa da su da alhẽri sa'an nan idan kun ƙĩ su, to akwai tsammãnin ku ƙi wani abu alhãli kuwa Allah Ya sanya wani alhẽri mai yawaa cikinsa.
20وَإِنْ أَرَدتُّمُ اسْتِبْدَالَ زَوْجٍ مَّكَانَ زَوْجٍ وَآتَيْتُمْ إِحْدَاهُنَّ قِنطَارًا فَلَا تَأْخُذُوا مِنْهُ شَيْئًا ۚ أَتَأْخُذُونَهُ بُهْتَانًا وَإِثْمًا مُّبِينًا
Kuma idan kun yi nufin musanya mãta a matsayin wata mãta, alhãli kuwa kun bai wa ɗayarsu ƙinɗari to kada ku karɓi kõme daga gare, shi, shin, zã ku karɓe shi da ƙarya da zunubi bãyyananne?
21وَكَيْفَ تَأْخُذُونَهُ وَقَدْ أَفْضَىٰ بَعْضُكُمْ إِلَىٰ بَعْضٍ وَأَخَذْنَ مِنكُم مِّيثَاقًا غَلِيظًا
Kuma yãyã zã ku karɓe shi alhãli kuwa, haƙĩƙa, sãshenkuyã sãdu zuwa ga sãshe, kuma sun riƙi alkawari mai kauri daga gare ku?
22وَلَا تَنكِحُوا مَا نَكَحَ آبَاؤُكُم مِّنَ النِّسَاءِ إِلَّا مَا قَدْ سَلَفَ ۚ إِنَّهُ كَانَ فَاحِشَةً وَمَقْتًا وَسَاءَ سَبِيلًا
Kuma kada ku auri abin da ubanninku suka aura daga mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne shi, ya kasance alfãsha da abin ƙyãma. Kuma ya mũnana ya zama hanya.
23حُرِّمَتْ عَلَيْكُمْ أُمَّهَاتُكُمْ وَبَنَاتُكُمْ وَأَخَوَاتُكُمْ وَعَمَّاتُكُمْ وَخَالَاتُكُمْ وَبَنَاتُ الْأَخِ وَبَنَاتُ الْأُخْتِ وَأُمَّهَاتُكُمُ اللَّاتِي أَرْضَعْنَكُمْ وَأَخَوَاتُكُم مِّنَ الرَّضَاعَةِ وَأُمَّهَاتُ نِسَائِكُمْ وَرَبَائِبُكُمُ اللَّاتِي فِي حُجُورِكُم مِّن نِّسَائِكُمُ اللَّاتِي دَخَلْتُم بِهِنَّ فَإِن لَّمْ تَكُونُوا دَخَلْتُم بِهِنَّ فَلَا جُنَاحَ عَلَيْكُمْ وَحَلَائِلُ أَبْنَائِكُمُ الَّذِينَ مِنْ أَصْلَابِكُمْ وَأَن تَجْمَعُوا بَيْنَ الْأُخْتَيْنِ إِلَّا مَا قَدْ سَلَفَ ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ غَفُورًا رَّحِيمًا
An haramta muku uwãyenku, da 'yã'yanku, da 'yan'uwanku mãtã, da goggonninku, da innoninku, da 'yã'yan ɗan'uwa, da 'ya'yan 'yar'uwa, da uwãyenku waɗanan da suka shãyar da ku mãma, da 'yan'uwanku mãtã na shan mãma, da uwãyen mãtanku, da agõlolinku waɗanda suke cikin ɗãkunanku daga mãtanku, waɗanda kuka yi duhũli da su, kuma idan ba ku yi duhũli da sũ ba, to, bãbu laifi a kanku, da mãtan 'yã'yanku waɗanda, suke daga tsatsonku, kuma kada ku haɗa tsakanin 'yan'uwa biyu mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne, Allah Yã kasance Mai gãfara ne Mai jin ƙai.
An-NisaJerin Alqur'ani
176Aya
MedinanRevelation
21Aya

Fassara — An-Nisa 21

Surah An-Nisa Aya 21 - Karatu, Saurara, Fassara, Hausa : Kuma yãyã zã ku karɓe shi alhãli kuwa, haƙĩƙa, sãshenkuyã…

Surah Aya 21/176 — Surah An-Nisa النساء (Medinan). Karatu Saurara Fassara (Hausa). Saurara: Surah An-Nisa Saurara, Surah An-Nisa Fassara, Surah An-Nisa mp3, Surah An-Nisa pdf. Aya 19–23. Da Hausa: العربية.




Al-Kur'ani


Tuesday, September 8, 2026

Don't forget us in your sincere prayers