سوره الرحمن به زبان هَوُسَ

  1. گوش دادن به سوره
  2. سورهای دیگر
  3. ترجمه سوره
قرآن کریم | ترجمه معانی قرآن | زبان هَوُسَ | سوره الرحمن | الرحمن - تعداد آیات آن 78 - شماره سوره در مصحف: 55 - معنی سوره به انگلیسی: The Most Merciful.

الرَّحْمَٰنُ(1)

 (Allah) Mai rahama.

عَلَّمَ الْقُرْآنَ(2)

 Yã sanar da Alƙur'ani.

خَلَقَ الْإِنسَانَ(3)

 Yã halitta mutum.

عَلَّمَهُ الْبَيَانَ(4)

 Yã sanar da shi bayãni (magana).

الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ(5)

 Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

وَالنَّجْمُ وَالشَّجَرُ يَسْجُدَانِ(6)

 Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

وَالسَّمَاءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ الْمِيزَانَ(7)

 Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

أَلَّا تَطْغَوْا فِي الْمِيزَانِ(8)

 Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

وَأَقِيمُوا الْوَزْنَ بِالْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا الْمِيزَانَ(9)

 Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

وَالْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ(10)

 Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

فِيهَا فَاكِهَةٌ وَالنَّخْلُ ذَاتُ الْأَكْمَامِ(11)

 A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

وَالْحَبُّ ذُو الْعَصْفِ وَالرَّيْحَانُ(12)

 Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(13)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?

خَلَقَ الْإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ كَالْفَخَّارِ(14)

 Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

وَخَلَقَ الْجَانَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ(15)

 Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(16)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

رَبُّ الْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ الْمَغْرِبَيْنِ(17)

 Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(18)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مَرَجَ الْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ(19)

 Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ(20)

 A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(21)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَخْرُجُ مِنْهُمَا اللُّؤْلُؤُ وَالْمَرْجَانُ(22)

 Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(23)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

وَلَهُ الْجَوَارِ الْمُنشَآتُ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ(24)

 Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(25)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ(26)

 Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ(27)

 Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(28)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَسْأَلُهُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِي شَأْنٍ(29)

 wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(30)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ الثَّقَلَانِ(31)

 Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(32)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَا مَعْشَرَ الْجِنِّ وَالْإِنسِ إِنِ اسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا مِنْ أَقْطَارِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ فَانفُذُوا ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَانٍ(33)

 Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(34)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ(35)

 Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(36)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فَإِذَا انشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدِّهَانِ(37)

 Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(38)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْأَلُ عَن ذَنبِهِ إِنسٌ وَلَا جَانٌّ(39)

 To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(40)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يُعْرَفُ الْمُجْرِمُونَ بِسِيمَاهُمْ فَيُؤْخَذُ بِالنَّوَاصِي وَالْأَقْدَامِ(41)

 zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(42)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا الْمُجْرِمُونَ(43)

 Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ آنٍ(44)

 Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(45)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ جَنَّتَانِ(46)

 Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(47)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

ذَوَاتَا أَفْنَانٍ(48)

 Mãsu rassan itãce.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(49)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ(50)

 A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(51)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِمَا مِن كُلِّ فَاكِهَةٍ زَوْجَانِ(52)

 A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(53)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ فُرُشٍ بَطَائِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى الْجَنَّتَيْنِ دَانٍ(54)

 Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(55)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِنَّ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ(56)

 A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(57)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

كَأَنَّهُنَّ الْيَاقُوتُ وَالْمَرْجَانُ(58)

 Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(59)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

هَلْ جَزَاءُ الْإِحْسَانِ إِلَّا الْإِحْسَانُ(60)

 Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(61)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ(62)

 Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(63)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مُدْهَامَّتَانِ(64)

 Mãsu duhun inuwa.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(65)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ(66)

 A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(67)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِمَا فَاكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ(68)

 A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(69)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِنَّ خَيْرَاتٌ حِسَانٌ(70)

 A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(71)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

حُورٌ مَّقْصُورَاتٌ فِي الْخِيَامِ(72)

 Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(73)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ(74)

 Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(75)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِيٍّ حِسَانٍ(76)

 Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ(77)

 To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

تَبَارَكَ اسْمُ رَبِّكَ ذِي الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ(78)

 Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.


سورهای بیشتر به زبان هَوُسَ:

سوره البقره آل عمران سوره نساء
سوره مائده سوره يوسف سوره ابراهيم
سوره حجر سوره کهف سوره مریم
سوره حج سوره قصص سوره عنکبوت
سوره سجده سوره یس سوره دخان
سوره فتح سوره حجرات سوره ق
سوره نجم سوره رحمن سوره واقعه
سوره حشر سوره ملک سوره حاقه
سوره انشقاق سوره أعلى سوره غاشية

دانلود سوره الرحمن با صدای معروف‌ترین قراء:

انتخاب خواننده برای گوش دادن و دانلود کامل سوره الرحمن با کیفیت بالا.
سوره الرحمن را با صدای احمد العجمی
أحمد العجمي
سوره الرحمن را با صدای ابراهيم الاخضر
ابراهيم الاخضر
سوره الرحمن را با صدای بندر بليلة
بندر بليلة
سوره الرحمن را با صدای خالد الجليل
خالد الجليل
سوره الرحمن را با صدای حاتم فريد الواعر
حاتم فريد الواعر
سوره الرحمن را با صدای خليفة الطنيجي
خليفة الطنيجي
سوره الرحمن را با صدای سعد الغامدي
سعد الغامدي
سوره الرحمن را با صدای سعود الشريم
سعود الشريم
سوره الرحمن را با صدای الشاطري
الشاطري
سوره الرحمن را با صدای صلاح ابوخاطر
صلاح بوخاطر
سوره الرحمن را با صدای عبد الباسط عبد الصمد
عبد الباسط
سوره الرحمن را با صدای عبد الرحمن العوسي
عبدالرحمن العوسي
سوره الرحمن را با صدای عبد الرشيد صوفي
عبد الرشيد صوفي
سوره الرحمن را با صدای عبد العزيز الزهراني
عبدالعزيز الزهراني
سوره الرحمن را با صدای عبد الله بصفر
عبد الله بصفر
سوره الرحمن را با صدای عبد الله عواد الجهني
عبد الله الجهني
سوره الرحمن را با صدای علي الحذيفي
علي الحذيفي
سوره الرحمن را با صدای علي جابر
علي جابر
سوره الرحمن را با صدای غسان الشوربجي
غسان الشوربجي
سوره الرحمن را با صدای فارس عباد
فارس عباد
سوره الرحمن را با صدای ماهر المعيقلي
ماهر المعيقلي
سوره الرحمن را با صدای محمد أيوب
محمد أيوب
سوره الرحمن را با صدای محمد المحيسني
محمد المحيسني
سوره الرحمن را با صدای محمد جبريل
محمد جبريل
سوره الرحمن را با صدای محمد صديق المنشاوي
المنشاوي
سوره الرحمن را با صدای الحصري
الحصري
سوره الرحمن را با صدای العفاسي
مشاري العفاسي
سوره الرحمن را با صدای ناصر القطامي
ناصر القطامي
سوره الرحمن را با صدای وديع اليمني
وديع اليمني
سوره الرحمن را با صدای ياسر الدوسري
ياسر الدوسري


Monday, May 13, 2024

به قرآن کریم چنگ بزنید