Surah Al-Qiyamah Larabci da Hausa

Karanta Surah Al-Qiyamah tare da cikakkiyar fassarar Hausa da sauti. Fassara aya bayan aya. (40 Aya — مكية). Al-Qiyamah Saurara, Al-Qiyamah Fassara, Al-Qiyamah mp3, Al-Qiyamah pdf.

Karanta da Saurara Surah Al-Qiyamah

🎧 Aya
M Mishary Rashid Alafasy
M Mahmoud Khalil Al-Husary
A Abdurrahman As-Sudais
M Mohamed Siddiq Al-Minshawi
A Abdul Basit Abdul Samad
A Ali Al-Hudhaify
A Ahmed ibn Ali al-Ajamy
A Abu Bakr Ash-Shaatree
M Muhammad Ayyoub
A Abdullah Basfar
A Abdullah Al-Juhani
M Maher Al Muaiqly
x1
لَا أُقْسِمُ بِيَوْمِ الْقِيَامَةِ ۝١
📖 Fassara Aya 1
Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
وَلَا أُقْسِمُ بِالنَّفْسِ اللَّوَّامَةِ ۝٢
📖 Fassara Aya 2
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُ ۝٣
📖 Fassara Aya 3
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
بَلَىٰ قَادِرِينَ عَلَىٰ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُ ۝٤
📖 Fassara Aya 4
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
بَلْ يُرِيدُ الْإِنسَانُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُ ۝٥
📖 Fassara Aya 5
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
يَسْأَلُ أَيَّانَ يَوْمُ الْقِيَامَةِ ۝٦
📖 Fassara Aya 6
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
فَإِذَا بَرِقَ الْبَصَرُ ۝٧
📖 Fassara Aya 7
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
وَخَسَفَ الْقَمَرُ ۝٨
📖 Fassara Aya 8
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
وَجُمِعَ الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ ۝٩
📖 Fassara Aya 9
Aka tãra rãnã da watã
يَقُولُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ الْمَفَرُّ ۝١٠
📖 Fassara Aya 10
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
كَلَّا لَا وَزَرَ ۝١١
📖 Fassara Aya 11
A'aha! bãbu mafaka.
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمُسْتَقَرُّ ۝١٢
📖 Fassara Aya 12
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
يُنَبَّأُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ ۝١٣
📖 Fassara Aya 13
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
بَلِ الْإِنسَانُ عَلَىٰ نَفْسِهِ بَصِيرَةٌ ۝١٤
📖 Fassara Aya 14
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُ ۝١٥
📖 Fassara Aya 15
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
لَا تُحَرِّكْ بِهِ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِ ۝١٦
📖 Fassara Aya 16
Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُ وَقُرْآنَهُ ۝١٧
📖 Fassara Aya 17
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
فَإِذَا قَرَأْنَاهُ فَاتَّبِعْ قُرْآنَهُ ۝١٨
📖 Fassara Aya 18
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُ ۝١٩
📖 Fassara Aya 19
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ الْعَاجِلَةَ ۝٢٠
📖 Fassara Aya 20
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
وَتَذَرُونَ الْآخِرَةَ ۝٢١
📖 Fassara Aya 21
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌ ۝٢٢
📖 Fassara Aya 22
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌ ۝٢٣
📖 Fassara Aya 23
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ بَاسِرَةٌ ۝٢٤
📖 Fassara Aya 24
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌ ۝٢٥
📖 Fassara Aya 25
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
كَلَّا إِذَا بَلَغَتِ التَّرَاقِيَ ۝٢٦
📖 Fassara Aya 26
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍ ۝٢٧
📖 Fassara Aya 27
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
وَظَنَّ أَنَّهُ الْفِرَاقُ ۝٢٨
📖 Fassara Aya 28
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
وَالْتَفَّتِ السَّاقُ بِالسَّاقِ ۝٢٩
📖 Fassara Aya 29
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمَسَاقُ ۝٣٠
📖 Fassara Aya 30
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ ۝٣١
📖 Fassara Aya 31
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ ۝٣٢
📖 Fassara Aya 32
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰ أَهْلِهِ يَتَمَطَّىٰ ۝٣٣
📖 Fassara Aya 33
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ ۝٣٤
📖 Fassara Aya 34
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ ۝٣٥
📖 Fassara Aya 35
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَن يُتْرَكَ سُدًى ۝٣٦
📖 Fassara Aya 36
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
أَلَمْ يَكُ نُطْفَةً مِّن مَّنِيٍّ يُمْنَىٰ ۝٣٧
📖 Fassara Aya 37
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
ثُمَّ كَانَ عَلَقَةً فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ ۝٣٨
📖 Fassara Aya 38
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
فَجَعَلَ مِنْهُ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ ۝٣٩
📖 Fassara Aya 39
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?
أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَادِرٍ عَلَىٰ أَن يُحْيِيَ الْمَوْتَىٰ ۝٤٠
📖 Fassara Aya 40
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?
← 74 Al-Qiyamah (75/114) 76 →
Karatu Surah Al-Qiyamah Hausa – Fassara da Audio

75القيامة Al-Qiyamah 📚 40 Aya مكية



Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers