Surah Al-Muddaththir Larabci da Hausa

Karanta Surah Al-Muddaththir tare da cikakkiyar fassarar Hausa da sauti. Fassara aya bayan aya. (56 Aya — مكية). Al-Muddaththir Saurara, Al-Muddaththir Fassara, Al-Muddaththir mp3, Al-Muddaththir pdf.

Karanta da Saurara Surah Al-Muddaththir

🎧 Aya
M Mishary Rashid Alafasy
M Mahmoud Khalil Al-Husary
A Abdurrahman As-Sudais
M Mohamed Siddiq Al-Minshawi
A Abdul Basit Abdul Samad
A Ali Al-Hudhaify
A Ahmed ibn Ali al-Ajamy
A Abu Bakr Ash-Shaatree
M Muhammad Ayyoub
A Abdullah Basfar
A Abdullah Al-Juhani
M Maher Al Muaiqly
x1
يَا أَيُّهَا الْمُدَّثِّرُ ۝١
📖 Fassara Aya 1
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
قُمْ فَأَنذِرْ ۝٢
📖 Fassara Aya 2
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ ۝٣
📖 Fassara Aya 3
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ ۝٤
📖 Fassara Aya 4
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
وَالرُّجْزَ فَاهْجُرْ ۝٥
📖 Fassara Aya 5
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ ۝٦
📖 Fassara Aya 6
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri
وَلِرَبِّكَ فَاصْبِرْ ۝٧
📖 Fassara Aya 7
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
فَإِذَا نُقِرَ فِي النَّاقُورِ ۝٨
📖 Fassara Aya 8
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.
فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍ يَوْمٌ عَسِيرٌ ۝٩
📖 Fassara Aya 9
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya
عَلَى الْكَافِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍ ۝١٠
📖 Fassara Aya 10
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.
ذَرْنِي وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًا ۝١١
📖 Fassara Aya 11
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,
وَجَعَلْتُ لَهُ مَالًا مَّمْدُودًا ۝١٢
📖 Fassara Aya 12
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya
وَبَنِينَ شُهُودًا ۝١٣
📖 Fassara Aya 13
Da ɗiyã halartattu,
وَمَهَّدتُّ لَهُ تَمْهِيدًا ۝١٤
📖 Fassara Aya 14
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ ۝١٥
📖 Fassara Aya 15
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!
كَلَّا ۖ إِنَّهُ كَانَ لِآيَاتِنَا عَنِيدًا ۝١٦
📖 Fassara Aya 16
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.
سَأُرْهِقُهُ صَعُودًا ۝١٧
📖 Fassara Aya 17
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
إِنَّهُ فَكَّرَ وَقَدَّرَ ۝١٨
📖 Fassara Aya 18
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)
فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ ۝١٩
📖 Fassara Aya 19
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ ۝٢٠
📖 Fassara Aya 20
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
ثُمَّ نَظَرَ ۝٢١
📖 Fassara Aya 21
Sa'an nan, ya yi tunãni
ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ ۝٢٢
📖 Fassara Aya 22
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
ثُمَّ أَدْبَرَ وَاسْتَكْبَرَ ۝٢٣
📖 Fassara Aya 23
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
فَقَالَ إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ يُؤْثَرُ ۝٢٤
📖 Fassara Aya 24
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
إِنْ هَٰذَا إِلَّا قَوْلُ الْبَشَرِ ۝٢٥
📖 Fassara Aya 25
"Wannan maganar mutum dai ce."
سَأُصْلِيهِ سَقَرَ ۝٢٦
📖 Fassara Aya 26
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
وَمَا أَدْرَاكَ مَا سَقَرُ ۝٢٧
📖 Fassara Aya 27
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
لَا تُبْقِي وَلَا تَذَرُ ۝٢٨
📖 Fassara Aya 28
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.
لَوَّاحَةٌ لِّلْبَشَرِ ۝٢٩
📖 Fassara Aya 29
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ ۝٣٠
📖 Fassara Aya 30
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.
وَمَا جَعَلْنَا أَصْحَابَ النَّارِ إِلَّا مَلَائِكَةً ۙ وَمَا جَعَلْنَا عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةً لِّلَّذِينَ كَفَرُوا لِيَسْتَيْقِنَ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ وَيَزْدَادَ الَّذِينَ آمَنُوا إِيمَانًا ۙ وَلَا يَرْتَابَ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ وَالْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ الَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٌ وَالْكَافِرُونَ مَاذَا أَرَادَ اللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلًا ۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ اللَّهُ مَن يَشَاءُ وَيَهْدِي مَن يَشَاءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ ۝٣١
📖 Fassara Aya 31
Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.
كَلَّا وَالْقَمَرِ ۝٣٢
📖 Fassara Aya 32
A'aha! Ina rantsuwa da watã.
وَاللَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ ۝٣٣
📖 Fassara Aya 33
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
وَالصُّبْحِ إِذَا أَسْفَرَ ۝٣٤
📖 Fassara Aya 34
Da sãfiya idan ta wãye.
إِنَّهَا لَإِحْدَى الْكُبَرِ ۝٣٥
📖 Fassara Aya 35
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
نَذِيرًا لِّلْبَشَرِ ۝٣٦
📖 Fassara Aya 36
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ ۝٣٧
📖 Fassara Aya 37
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.
كُلُّ نَفْسٍ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ ۝٣٨
📖 Fassara Aya 38
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.
إِلَّا أَصْحَابَ الْيَمِينِ ۝٣٩
📖 Fassara Aya 39
Fãce mutãnen dãma.
فِي جَنَّاتٍ يَتَسَاءَلُونَ ۝٤٠
📖 Fassara Aya 40
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.
عَنِ الْمُجْرِمِينَ ۝٤١
📖 Fassara Aya 41
Game da mãsu laifi.
مَا سَلَكَكُمْ فِي سَقَرَ ۝٤٢
📖 Fassara Aya 42
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"
قَالُوا لَمْ نَكُ مِنَ الْمُصَلِّينَ ۝٤٣
📖 Fassara Aya 43
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."
وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ الْمِسْكِينَ ۝٤٤
📖 Fassara Aya 44
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."
وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ الْخَائِضِينَ ۝٤٥
📖 Fassara Aya 45
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ الدِّينِ ۝٤٦
📖 Fassara Aya 46
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."
حَتَّىٰ أَتَانَا الْيَقِينُ ۝٤٧
📖 Fassara Aya 47
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَاعَةُ الشَّافِعِينَ ۝٤٨
📖 Fassara Aya 48
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
فَمَا لَهُمْ عَنِ التَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ ۝٤٩
📖 Fassara Aya 49
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
كَأَنَّهُمْ حُمُرٌ مُّسْتَنفِرَةٌ ۝٥٠
📖 Fassara Aya 50
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍ ۝٥١
📖 Fassara Aya 51
Sun gudu daga zãki.
بَلْ يُرِيدُ كُلُّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًا مُّنَشَّرَةً ۝٥٢
📖 Fassara Aya 52
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa
كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ الْآخِرَةَ ۝٥٣
📖 Fassara Aya 53
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
كَلَّا إِنَّهُ تَذْكِرَةٌ ۝٥٤
📖 Fassara Aya 54
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
فَمَن شَاءَ ذَكَرَهُ ۝٥٥
📖 Fassara Aya 55
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّا أَن يَشَاءَ اللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ التَّقْوَىٰ وَأَهْلُ الْمَغْفِرَةِ ۝٥٦
📖 Fassara Aya 56
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.
← 73 Al-Muddaththir (74/114) 75 →
Karatu Surah Al-Muddaththir Hausa – Fassara da Audio

74المدثر Al-Muddaththir 📚 56 Aya مكية

Aya bayan aya – Surah Al-Muddaththir — 56 Aya




Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers