سوره دخان به زبان هَوُسَ

  1. گوش دادن به سوره
  2. سورهای دیگر
  3. ترجمه سوره
قرآن کریم | ترجمه معانی قرآن | زبان هَوُسَ | سوره دخان | الدخان - تعداد آیات آن 59 - شماره سوره در مصحف: 44 - معنی سوره به انگلیسی: The Smoke.

حم(1)

 Ḥ. M̃.

وَالْكِتَابِ الْمُبِينِ(2)

 Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.

إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةٍ مُّبَارَكَةٍ ۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ(3)

 Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.

فِيهَا يُفْرَقُ كُلُّ أَمْرٍ حَكِيمٍ(4)

 A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.

أَمْرًا مِّنْ عِندِنَا ۚ إِنَّا كُنَّا مُرْسِلِينَ(5)

 Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.

رَحْمَةً مِّن رَّبِّكَ ۚ إِنَّهُ هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ(6)

 Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.

رَبِّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ(7)

 (Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).

لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ يُحْيِي وَيُمِيتُ ۖ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ(8)

 Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.

بَلْ هُمْ فِي شَكٍّ يَلْعَبُونَ(9)

 A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.

فَارْتَقِبْ يَوْمَ تَأْتِي السَّمَاءُ بِدُخَانٍ مُّبِينٍ(10)

 Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.

يَغْشَى النَّاسَ ۖ هَٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٌ(11)

 Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.

رَّبَّنَا اكْشِفْ عَنَّا الْعَذَابَ إِنَّا مُؤْمِنُونَ(12)

 Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.

أَنَّىٰ لَهُمُ الذِّكْرَىٰ وَقَدْ جَاءَهُمْ رَسُولٌ مُّبِينٌ(13)

 Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?

ثُمَّ تَوَلَّوْا عَنْهُ وَقَالُوا مُعَلَّمٌ مَّجْنُونٌ(14)

 Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."

إِنَّا كَاشِفُو الْعَذَابِ قَلِيلًا ۚ إِنَّكُمْ عَائِدُونَ(15)

 Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).

يَوْمَ نَبْطِشُ الْبَطْشَةَ الْكُبْرَىٰ إِنَّا مُنتَقِمُونَ(16)

 Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.

۞ وَلَقَدْ فَتَنَّا قَبْلَهُمْ قَوْمَ فِرْعَوْنَ وَجَاءَهُمْ رَسُولٌ كَرِيمٌ(17)

 Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.

أَنْ أَدُّوا إِلَيَّ عِبَادَ اللَّهِ ۖ إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ(18)

 (Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."

وَأَن لَّا تَعْلُوا عَلَى اللَّهِ ۖ إِنِّي آتِيكُم بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ(19)

 "Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."

وَإِنِّي عُذْتُ بِرَبِّي وَرَبِّكُمْ أَن تَرْجُمُونِ(20)

 "Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."

وَإِن لَّمْ تُؤْمِنُوا لِي فَاعْتَزِلُونِ(21)

 "Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."

فَدَعَا رَبَّهُ أَنَّ هَٰؤُلَاءِ قَوْمٌ مُّجْرِمُونَ(22)

 Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.

فَأَسْرِ بِعِبَادِي لَيْلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ(23)

 (Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"

وَاتْرُكِ الْبَحْرَ رَهْوًا ۖ إِنَّهُمْ جُندٌ مُّغْرَقُونَ(24)

 "Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."

كَمْ تَرَكُوا مِن جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ(25)

 Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.

وَزُرُوعٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍ(26)

 Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.

وَنَعْمَةٍ كَانُوا فِيهَا فَاكِهِينَ(27)

 Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.

كَذَٰلِكَ ۖ وَأَوْرَثْنَاهَا قَوْمًا آخَرِينَ(28)

 Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.

فَمَا بَكَتْ عَلَيْهِمُ السَّمَاءُ وَالْأَرْضُ وَمَا كَانُوا مُنظَرِينَ(29)

 Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.

وَلَقَدْ نَجَّيْنَا بَنِي إِسْرَائِيلَ مِنَ الْعَذَابِ الْمُهِينِ(30)

 Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.

مِن فِرْعَوْنَ ۚ إِنَّهُ كَانَ عَالِيًا مِّنَ الْمُسْرِفِينَ(31)

 Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.

وَلَقَدِ اخْتَرْنَاهُمْ عَلَىٰ عِلْمٍ عَلَى الْعَالَمِينَ(32)

 Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.

وَآتَيْنَاهُم مِّنَ الْآيَاتِ مَا فِيهِ بَلَاءٌ مُّبِينٌ(33)

 Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna

إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَيَقُولُونَ(34)

 Lalle waɗannan mutãne, haƙĩka, sunã cẽwa,

إِنْ هِيَ إِلَّا مَوْتَتُنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُنشَرِينَ(35)

 "Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."

فَأْتُوا بِآبَائِنَا إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ(36)

 "Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."

أَهُمْ خَيْرٌ أَمْ قَوْمُ تُبَّعٍ وَالَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ أَهْلَكْنَاهُمْ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا مُجْرِمِينَ(37)

 shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.

وَمَا خَلَقْنَا السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا لَاعِبِينَ(38)

 Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.

مَا خَلَقْنَاهُمَا إِلَّا بِالْحَقِّ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ(39)

 Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.

إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ مِيقَاتُهُمْ أَجْمَعِينَ(40)

 Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.

يَوْمَ لَا يُغْنِي مَوْلًى عَن مَّوْلًى شَيْئًا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ(41)

 Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.

إِلَّا مَن رَّحِمَ اللَّهُ ۚ إِنَّهُ هُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ(42)

 fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

إِنَّ شَجَرَتَ الزَّقُّومِ(43)

 Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),

طَعَامُ الْأَثِيمِ(44)

 Ita ce abincin mai laifi.

كَالْمُهْلِ يَغْلِي فِي الْبُطُونِ(45)

 Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.

كَغَلْيِ الْحَمِيمِ(46)

 Kamar tafasar ruwan zãfi.

خُذُوهُ فَاعْتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَاءِ الْجَحِيمِ(47)

 (A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."

ثُمَّ صُبُّوا فَوْقَ رَأْسِهِ مِنْ عَذَابِ الْحَمِيمِ(48)

 "Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."

ذُقْ إِنَّكَ أَنتَ الْعَزِيزُ الْكَرِيمُ(49)

 (A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"

إِنَّ هَٰذَا مَا كُنتُم بِهِ تَمْتَرُونَ(50)

 "Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."

إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٍ(51)

 Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.

فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ(52)

 A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.

يَلْبَسُونَ مِن سُندُسٍ وَإِسْتَبْرَقٍ مُّتَقَابِلِينَ(53)

 Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.

كَذَٰلِكَ وَزَوَّجْنَاهُم بِحُورٍ عِينٍ(54)

 Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.

يَدْعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَاكِهَةٍ آمِنِينَ(55)

 Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).

لَا يَذُوقُونَ فِيهَا الْمَوْتَ إِلَّا الْمَوْتَةَ الْأُولَىٰ ۖ وَوَقَاهُمْ عَذَابَ الْجَحِيمِ(56)

 Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.

فَضْلًا مِّن رَّبِّكَ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ(57)

 Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.

فَإِنَّمَا يَسَّرْنَاهُ بِلِسَانِكَ لَعَلَّهُمْ يَتَذَكَّرُونَ(58)

 Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.

فَارْتَقِبْ إِنَّهُم مُّرْتَقِبُونَ(59)

 Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.


سورهای بیشتر به زبان هَوُسَ:

سوره البقره آل عمران سوره نساء
سوره مائده سوره يوسف سوره ابراهيم
سوره حجر سوره کهف سوره مریم
سوره حج سوره قصص سوره عنکبوت
سوره سجده سوره یس سوره دخان
سوره فتح سوره حجرات سوره ق
سوره نجم سوره رحمن سوره واقعه
سوره حشر سوره ملک سوره حاقه
سوره انشقاق سوره أعلى سوره غاشية

دانلود سوره دخان با صدای معروف‌ترین قراء:

انتخاب خواننده برای گوش دادن و دانلود کامل سوره دخان با کیفیت بالا.
سوره دخان را با صدای احمد العجمی
أحمد العجمي
سوره دخان را با صدای ابراهيم الاخضر
ابراهيم الاخضر
سوره دخان را با صدای بندر بليلة
بندر بليلة
سوره دخان را با صدای خالد الجليل
خالد الجليل
سوره دخان را با صدای حاتم فريد الواعر
حاتم فريد الواعر
سوره دخان را با صدای خليفة الطنيجي
خليفة الطنيجي
سوره دخان را با صدای سعد الغامدي
سعد الغامدي
سوره دخان را با صدای سعود الشريم
سعود الشريم
سوره دخان را با صدای الشاطري
الشاطري
سوره دخان را با صدای صلاح ابوخاطر
صلاح بوخاطر
سوره دخان را با صدای عبد الباسط عبد الصمد
عبد الباسط
سوره دخان را با صدای عبد الرحمن العوسي
عبدالرحمن العوسي
سوره دخان را با صدای عبد الرشيد صوفي
عبد الرشيد صوفي
سوره دخان را با صدای عبد العزيز الزهراني
عبدالعزيز الزهراني
سوره دخان را با صدای عبد الله بصفر
عبد الله بصفر
سوره دخان را با صدای عبد الله عواد الجهني
عبد الله الجهني
سوره دخان را با صدای علي الحذيفي
علي الحذيفي
سوره دخان را با صدای علي جابر
علي جابر
سوره دخان را با صدای غسان الشوربجي
غسان الشوربجي
سوره دخان را با صدای فارس عباد
فارس عباد
سوره دخان را با صدای ماهر المعيقلي
ماهر المعيقلي
سوره دخان را با صدای محمد أيوب
محمد أيوب
سوره دخان را با صدای محمد المحيسني
محمد المحيسني
سوره دخان را با صدای محمد جبريل
محمد جبريل
سوره دخان را با صدای محمد صديق المنشاوي
المنشاوي
سوره دخان را با صدای الحصري
الحصري
سوره دخان را با صدای العفاسي
مشاري العفاسي
سوره دخان را با صدای ناصر القطامي
ناصر القطامي
سوره دخان را با صدای وديع اليمني
وديع اليمني
سوره دخان را با صدای ياسر الدوسري
ياسر الدوسري


Sunday, May 12, 2024

به قرآن کریم چنگ بزنید