Surah As-Saffat Larabci da Hausa
Karanta Surah As-Saffat tare da cikakkiyar fassarar Hausa da sauti. Fassara aya bayan aya. (182 Aya — مكية). As-Saffat Saurara, As-Saffat Fassara, As-Saffat mp3, As-Saffat pdf.Karanta da Saurara Surah As-Saffat
🎧 Aya
M
Mishary Rashid Alafasy
✓
Mishary Rashid Alafasy
✓
M
Mahmoud Khalil Al-Husary
✓
Mahmoud Khalil Al-Husary
✓
A
Abdurrahman As-Sudais
✓
Abdurrahman As-Sudais
✓
M
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
✓
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
✓
A
Abdul Basit Abdul Samad
✓
Abdul Basit Abdul Samad
✓
A
Ali Al-Hudhaify
✓
Ali Al-Hudhaify
✓
A
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
✓
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
✓
A
Abu Bakr Ash-Shaatree
✓
Abu Bakr Ash-Shaatree
✓
M
Muhammad Ayyoub
✓
Muhammad Ayyoub
✓
A
Abdullah Basfar
✓
Abdullah Basfar
✓
A
Abdullah Al-Juhani
✓
Abdullah Al-Juhani
✓
M
Maher Al Muaiqly
✓
Maher Al Muaiqly
✓
—
x1
وَالصَّافَّاتِ صَفًّا ١
📖 Fassara
Aya 1
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِ ٥
📖 Fassara
Aya 5
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِ ٦
📖 Fassara
Aya 6
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍ ٧
📖 Fassara
Aya 7
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلَإِ الْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ ٨
📖 Fassara
Aya 8
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ ٩
📖 Fassara
Aya 9
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
إِلَّا مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌ ١٠
📖 Fassara
Aya 10
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا ۚ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍ ١١
📖 Fassara
Aya 11
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَ ١٤
📖 Fassara
Aya 14
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
وَقَالُوا إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ ١٥
📖 Fassara
Aya 15
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ ١٦
📖 Fassara
Aya 16
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ ١٩
📖 Fassara
Aya 19
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ الدِّينِ ٢٠
📖 Fassara
Aya 20
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
هَٰذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ ٢١
📖 Fassara
Aya 21
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
۞ احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَ ٢٢
📖 Fassara
Aya 22
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
مِن دُونِ اللَّهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطِ الْجَحِيمِ ٢٣
📖 Fassara
Aya 23
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَ ٢٤
📖 Fassara
Aya 24
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ ٢٧
📖 Fassara
Aya 27
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ ٢٨
📖 Fassara
Aya 28
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ ٢٩
📖 Fassara
Aya 29
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ ٣٠
📖 Fassara
Aya 30
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ ٣١
📖 Fassara
Aya 31
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ ٣٢
📖 Fassara
Aya 32
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ ٣٣
📖 Fassara
Aya 33
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَ ٣٤
📖 Fassara
Aya 34
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَٰهَ إِلَّا اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ ٣٥
📖 Fassara
Aya 35
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍ ٣٦
📖 Fassara
Aya 36
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ ٣٧
📖 Fassara
Aya 37
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ ٣٨
📖 Fassara
Aya 38
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ ٣٩
📖 Fassara
Aya 39
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
فَوَاكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ ٤٢
📖 Fassara
Aya 42
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ ٤٥
📖 Fassara
Aya 45
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ ٤٧
📖 Fassara
Aya 47
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌ ٤٨
📖 Fassara
Aya 48
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ ٥٠
📖 Fassara
Aya 50
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌ ٥١
📖 Fassara
Aya 51
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنَ الْمُصَدِّقِينَ ٥٢
📖 Fassara
Aya 52
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَدِينُونَ ٥٣
📖 Fassara
Aya 53
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ ٥٤
📖 Fassara
Aya 54
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاءِ الْجَحِيمِ ٥٥
📖 Fassara
Aya 55
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
قَالَ تَاللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ ٥٦
📖 Fassara
Aya 56
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَ ٥٧
📖 Fassara
Aya 57
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
إِلَّا مَوْتَتَنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ ٥٩
📖 Fassara
Aya 59
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ ٦٠
📖 Fassara
Aya 60
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ الْعَامِلُونَ ٦١
📖 Fassara
Aya 61
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِ ٦٢
📖 Fassara
Aya 62
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَ ٦٣
📖 Fassara
Aya 63
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِ ٦٤
📖 Fassara
Aya 64
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُءُوسُ الشَّيَاطِينِ ٦٥
📖 Fassara
Aya 65
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ ٦٦
📖 Fassara
Aya 66
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ ٦٧
📖 Fassara
Aya 67
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ ٦٨
📖 Fassara
Aya 68
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ ٧٠
📖 Fassara
Aya 70
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الْأَوَّلِينَ ٧١
📖 Fassara
Aya 71
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ ٧٢
📖 Fassara
Aya 72
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَ ٧٣
📖 Fassara
Aya 73
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَ ٧٥
📖 Fassara
Aya 75
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ ٧٦
📖 Fassara
Aya 76
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمُ الْبَاقِينَ ٧٧
📖 Fassara
Aya 77
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ ٧٨
📖 Fassara
Aya 78
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
سَلَامٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَ ٧٩
📖 Fassara
Aya 79
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ ٨٠
📖 Fassara
Aya 80
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
۞ وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَ ٨٣
📖 Fassara
Aya 83
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ ٨٤
📖 Fassara
Aya 84
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَ ٨٥
📖 Fassara
Aya 85
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللَّهِ تُرِيدُونَ ٨٦
📖 Fassara
Aya 86
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ ٨٧
📖 Fassara
Aya 87
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِ ٨٨
📖 Fassara
Aya 88
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَ ٩٠
📖 Fassara
Aya 90
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
فَرَاغَ إِلَىٰ آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ ٩١
📖 Fassara
Aya 91
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِ ٩٣
📖 Fassara
Aya 93
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَ ٩٤
📖 Fassara
Aya 94
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ ٩٥
📖 Fassara
Aya 95
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
وَاللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ ٩٦
📖 Fassara
Aya 96
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِ ٩٧
📖 Fassara
Aya 97
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الْأَسْفَلِينَ ٩٨
📖 Fassara
Aya 98
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهْدِينِ ٩٩
📖 Fassara
Aya 99
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ ١٠٠
📖 Fassara
Aya 100
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلَامٍ حَلِيمٍ ١٠١
📖 Fassara
Aya 101
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَىٰ فِي الْمَنَامِ أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللَّهُ مِنَ الصَّابِرِينَ ١٠٢
📖 Fassara
Aya 102
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِ ١٠٣
📖 Fassara
Aya 103
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ ١٠٥
📖 Fassara
Aya 105
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْبَلَاءُ الْمُبِينُ ١٠٦
📖 Fassara
Aya 106
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ ١٠٧
📖 Fassara
Aya 107
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ ١٠٨
📖 Fassara
Aya 108
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَ ١١٢
📖 Fassara
Aya 112
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰ إِسْحَاقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌ ١١٣
📖 Fassara
Aya 113
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ ١١٤
📖 Fassara
Aya 114
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ ١١٥
📖 Fassara
Aya 115
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ ١١٦
📖 Fassara
Aya 116
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَ ١١٧
📖 Fassara
Aya 117
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
وَهَدَيْنَاهُمَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ ١١٨
📖 Fassara
Aya 118
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِي الْآخِرِينَ ١١٩
📖 Fassara
Aya 119
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ ١٢١
📖 Fassara
Aya 121
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ ١٢٣
📖 Fassara
Aya 123
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَلَا تَتَّقُونَ ١٢٤
📖 Fassara
Aya 124
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ الْخَالِقِينَ ١٢٥
📖 Fassara
Aya 125
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
اللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ ١٢٦
📖 Fassara
Aya 126
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ ١٢٧
📖 Fassara
Aya 127
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ ١٢٩
📖 Fassara
Aya 129
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ ١٣١
📖 Fassara
Aya 131
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ الْمُرْسَلِينَ ١٣٣
📖 Fassara
Aya 133
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ نَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ ١٣٤
📖 Fassara
Aya 134
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ ١٣٥
📖 Fassara
Aya 135
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ ١٣٧
📖 Fassara
Aya 137
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
وَبِاللَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ ١٣٨
📖 Fassara
Aya 138
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ ١٣٩
📖 Fassara
Aya 139
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ أَبَقَ إِلَى الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ ١٤٠
📖 Fassara
Aya 140
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ الْمُدْحَضِينَ ١٤١
📖 Fassara
Aya 141
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
فَالْتَقَمَهُ الْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌ ١٤٢
📖 Fassara
Aya 142
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
فَلَوْلَا أَنَّهُ كَانَ مِنَ الْمُسَبِّحِينَ ١٤٣
📖 Fassara
Aya 143
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
لَلَبِثَ فِي بَطْنِهِ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ ١٤٤
📖 Fassara
Aya 144
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
۞ فَنَبَذْنَاهُ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ سَقِيمٌ ١٤٥
📖 Fassara
Aya 145
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
وَأَنبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍ ١٤٦
📖 Fassara
Aya 146
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
وَأَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ مِائَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ ١٤٧
📖 Fassara
Aya 147
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
فَآمَنُوا فَمَتَّعْنَاهُمْ إِلَىٰ حِينٍ ١٤٨
📖 Fassara
Aya 148
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
فَاسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ الْبَنَاتُ وَلَهُمُ الْبَنُونَ ١٤٩
📖 Fassara
Aya 149
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
أَمْ خَلَقْنَا الْمَلَائِكَةَ إِنَاثًا وَهُمْ شَاهِدُونَ ١٥٠
📖 Fassara
Aya 150
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
أَلَا إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ ١٥١
📖 Fassara
Aya 151
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
وَلَدَ اللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَ ١٥٢
📖 Fassara
Aya 152
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
أَصْطَفَى الْبَنَاتِ عَلَى الْبَنِينَ ١٥٣
📖 Fassara
Aya 153
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ ١٥٤
📖 Fassara
Aya 154
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
فَأْتُوا بِكِتَابِكُمْ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ ١٥٧
📖 Fassara
Aya 157
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
وَجَعَلُوا بَيْنَهُ وَبَيْنَ الْجِنَّةِ نَسَبًا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ الْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ ١٥٨
📖 Fassara
Aya 158
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ ١٥٩
📖 Fassara
Aya 159
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ الْجَحِيمِ ١٦٣
📖 Fassara
Aya 163
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
وَمَا مِنَّا إِلَّا لَهُ مَقَامٌ مَّعْلُومٌ ١٦٤
📖 Fassara
Aya 164
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
وَإِنَّا لَنَحْنُ الصَّافُّونَ ١٦٥
📖 Fassara
Aya 165
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
وَإِنَّا لَنَحْنُ الْمُسَبِّحُونَ ١٦٦
📖 Fassara
Aya 166
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنَ الْأَوَّلِينَ ١٦٨
📖 Fassara
Aya 168
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
لَكُنَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ ١٦٩
📖 Fassara
Aya 169
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
فَكَفَرُوا بِهِ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ ١٧٠
📖 Fassara
Aya 170
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا الْمُرْسَلِينَ ١٧١
📖 Fassara
Aya 171
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ الْغَالِبُونَ ١٧٣
📖 Fassara
Aya 173
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ ١٧٤
📖 Fassara
Aya 174
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ ١٧٥
📖 Fassara
Aya 175
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَاءَ صَبَاحُ الْمُنذَرِينَ ١٧٧
📖 Fassara
Aya 177
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ ١٧٨
📖 Fassara
Aya 178
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ ١٧٩
📖 Fassara
Aya 179
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
سُبْحَانَ رَبِّكَ رَبِّ الْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ ١٨٠
📖 Fassara
Aya 180
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
وَالْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ ١٨٢
📖 Fassara
Aya 182
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
Karatu Surah As-Saffat Hausa – Fassara da Audio
Al-Kur'ani
Tuesday, August 18, 2026
Don't forget us in your sincere prayers

