Aal-Imran · 77/200
Fassara Rubutun sauti — Surah Aal-Imran
إِنَّ الَّذِينَ يَشْتَرُونَ بِعَهْدِ اللَّهِ وَأَيْمَانِهِمْ ثَمَنًا قَلِيلًا أُولَٰئِكَ لَا خَلَاقَ لَهُمْ فِي الْآخِرَةِ وَلَا يُكَلِّمُهُمُ اللَّهُ وَلَا يَنظُرُ إِلَيْهِمْ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَلَا يُزَكِّيهِمْ وَلَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ ۝٧٧
Innal lazeena yashtaroona bi`ahdil laahi wa aymaanihim samanan qaleelan ulaaa`ika laa khalaaqa lahum fil Aakhirati wa laa yukallimuhumul laahu wa laa yanzuru ilaihim Yawmal Qiyaamati wa laa yuzakkeehim wa lahum `azabun `aleem
📖 Da Hausa
Lalle ne waɗanda suke sayen 'yan tamani kaɗan da alkawarin Allah da rantsuwõyinsu, waɗannan bãbu wani rabo a gare su a Lãhira, Kuma Allah bã Ya yin magana da su, kuma bã Ya dũbi zuwa gare su, a Rãnar ¡iyãma, kuma bã Ya tsarkake su, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.

🎧 Saurara
📜

Fassara — Tafsir

Ma’anonin Kalmomin Ayar:

  • "يَشْتَرُونَ": suna sayen, wato suna musanya.
  • "بِعَهْدِ اللَّهِ": da alkawarin Allah wanda ya ɗauka a kansu, kamar neman bin littattafansa da manzanninsa.
  • "وَأَيْمَانِهِمْ": da rantsuwowinsu na ƙarya da suke yi don su ci dukiyar mutane.
  • "ثَمَنًا قَلِيلًا": da ɗan kuɗi kaɗan na dukiyar duniya.
  • "لَا خَلَاقَ لَهُمْ": babu wani rabo ko sa’a a gare su.
  • "وَلَا يُزَكِّيهِمْ": kuma ba zai tsarkake su ba daga ƙazantar zunubai.

Fassarar Ayar:

Lalle ne waɗanda suke musanya alkawarin Allah da ya ɗauka a kansu, da kuma rantsuwowinsu na ƙarya, da ɗan kuɗi kaɗan na dukiyar duniya, waɗannan babu wani rabo a gare su a Lahira, kuma Allah ba zai yi musu magana ba da abin da zai faranta musu rai, kuma ba zai dube su ba da idon rahama a Ranar Kiyama, domin ya yi musu fushi, kuma ba zai tsarkake su ba daga ƙazantar zunubai da kafirci, kuma suna da azaba mai raɗaɗi a gare su saboda abin da suka aikata.

Fa’idodin Ayar:

  1. Nuna girman darajar alkawari da riƙon amana, kuma cewa sayar da su don bukatar duniya babban laifi ne.
  2. Tsoratarwa ga masu cin amana da yin rantsuwa na ƙarya don cin dukiyar mutane, cewa za su gamu da azaba mai zafi a Lahira.
  3. Ƙarfafa muminai su riƙa gaskiya da aminci, su kauce wa duk wani abin da zai kai su ga fushin Allah da rashin jinƙai a Ranar Kiyama.
  4. Nuna cewa Allah ba ya kallon mutane da idon rahama sai waɗanda suka tsarkaka daga zunubai, don haka mu yi ƙoƙari mu tsarkake kanmu ta hanyar imani da ayyukan ƙwarai.


📜 Aya 75-79 — Surah Aal-Imran

75۞ وَمِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ مَنْ إِن تَأْمَنْهُ بِقِنطَارٍ يُؤَدِّهِ إِلَيْكَ وَمِنْهُم مَّنْ إِن تَأْمَنْهُ بِدِينَارٍ لَّا يُؤَدِّهِ إِلَيْكَ إِلَّا مَا دُمْتَ عَلَيْهِ قَائِمًا ۗ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمْ قَالُوا لَيْسَ عَلَيْنَا فِي الْأُمِّيِّينَ سَبِيلٌ وَيَقُولُونَ عَلَى اللَّهِ الْكَذِبَ وَهُمْ يَعْلَمُونَ
Kuma daga Mutãnen Littãfi akwai wanda yake idan ka bã shi amãnar kinɗãri, zai bãyar da shi gare ka, kuma daga gare su akwai wanda idan ka bã shi amãnar dĩnari, bã zai bãyar da shi gare ka ba, fãce idan kã dawwama a kansa kanã tsaye. Wannan kuwa, dõmin lalle ne sũ sun ce, "Bãbu laifi a kanmu a cikin Ummiyyai." Suna faɗar ƙarya ga Allah, alhãli kuwa suna sane.
76بَلَىٰ مَنْ أَوْفَىٰ بِعَهْدِهِ وَاتَّقَىٰ فَإِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ الْمُتَّقِينَ
Na'am! Wanda ya cika alkawarinsa, kuma ya yi taƙawa, to, lalle ne Allah yana son mãsu taƙawa.
77إِنَّ الَّذِينَ يَشْتَرُونَ بِعَهْدِ اللَّهِ وَأَيْمَانِهِمْ ثَمَنًا قَلِيلًا أُولَٰئِكَ لَا خَلَاقَ لَهُمْ فِي الْآخِرَةِ وَلَا يُكَلِّمُهُمُ اللَّهُ وَلَا يَنظُرُ إِلَيْهِمْ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَلَا يُزَكِّيهِمْ وَلَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Lalle ne waɗanda suke sayen 'yan tamani kaɗan da alkawarin Allah da rantsuwõyinsu, waɗannan bãbu wani rabo a gare su a Lãhira, Kuma Allah bã Ya yin magana da su, kuma bã Ya dũbi zuwa gare su, a Rãnar ¡iyãma, kuma bã Ya tsarkake su, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.
78وَإِنَّ مِنْهُمْ لَفَرِيقًا يَلْوُونَ أَلْسِنَتَهُم بِالْكِتَابِ لِتَحْسَبُوهُ مِنَ الْكِتَابِ وَمَا هُوَ مِنَ الْكِتَابِ وَيَقُولُونَ هُوَ مِنْ عِندِ اللَّهِ وَمَا هُوَ مِنْ عِندِ اللَّهِ وَيَقُولُونَ عَلَى اللَّهِ الْكَذِبَ وَهُمْ يَعْلَمُونَ
Kuma lalle ne, daga gare su akwai wata ƙungiya suna karkatar da harsunansu da Littãfi dõmin ku yi zaton sa daga Littãfin, alhãli kuwa bã shi daga Littãfin. Kuma suna cẽwa: "Shi daga wurinAllah yake." Alhãli kuwa shi, bã daga wurin Allah yake ba. Sunã faɗar ƙarya ga Allah, alhãli kuwa sunã sane.
79مَا كَانَ لِبَشَرٍ أَن يُؤْتِيَهُ اللَّهُ الْكِتَابَ وَالْحُكْمَ وَالنُّبُوَّةَ ثُمَّ يَقُولَ لِلنَّاسِ كُونُوا عِبَادًا لِّي مِن دُونِ اللَّهِ وَلَٰكِن كُونُوا رَبَّانِيِّينَ بِمَا كُنتُمْ تُعَلِّمُونَ الْكِتَابَ وَبِمَا كُنتُمْ تَدْرُسُونَ
Ba ya yiwuwa ga wani mutum, Allah Ya bã shi Littãfi da hukunci da Annabci, sa'an nan kuma ya ce wa mutãne: "Ku kasance bãyi gare ni, baicin Allah." Amma (zai ce): "Ku kasance mãsu aikin ibãda da abin da kuka kasance kuna karantar da Littãfin, kuma da abin da kuka kasance kuna karantãwa."
Aal-ImranJerin Alqur'ani
200Aya
MedinanRevelation
77Aya

Fassara — Aal-Imran 77

Surah Aal-Imran Aya 77 - Karatu, Saurara, Fassara, Hausa : Lalle ne waɗanda suke sayen 'yan tamani kaɗan da alkawarin…

Surah Aya 77/200 — Surah Aal-Imran آل عمران (Medinan). Karatu Saurara Fassara (Hausa). Saurara: Surah Aal-Imran Saurara, Surah Aal-Imran Fassara, Surah Aal-Imran mp3, Surah Aal-Imran pdf. Aya 75–79. Da Hausa: العربية.




Al-Kur'ani


Monday, September 7, 2026

Don't forget us in your sincere prayers