Surah Al-Haqqah Larabci da Hausa

Karanta Surah Al-Haqqah tare da cikakkiyar fassarar Hausa da sauti. Fassara aya bayan aya. (52 Aya — مكية). Al-Haqqah Saurara, Al-Haqqah Fassara, Al-Haqqah mp3, Al-Haqqah pdf.

Karanta da Saurara Surah Al-Haqqah

🎧 Aya
M Mishary Rashid Alafasy
M Mahmoud Khalil Al-Husary
A Abdurrahman As-Sudais
M Mohamed Siddiq Al-Minshawi
A Abdul Basit Abdul Samad
A Ali Al-Hudhaify
A Ahmed ibn Ali al-Ajamy
A Abu Bakr Ash-Shaatree
M Muhammad Ayyoub
A Abdullah Basfar
A Abdullah Al-Juhani
M Maher Al Muaiqly
x1
الْحَاقَّةُ ۝١
📖 Fassara Aya 1
Kiran gaskiya!
مَا الْحَاقَّةُ ۝٢
📖 Fassara Aya 2
Mẽne ne kiran gaskiya?
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحَاقَّةُ ۝٣
📖 Fassara Aya 3
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌ بِالْقَارِعَةِ ۝٤
📖 Fassara Aya 4
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا بِالطَّاغِيَةِ ۝٥
📖 Fassara Aya 5
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ ۝٦
📖 Fassara Aya 6
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَانِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ ۝٧
📖 Fassara Aya 7
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّن بَاقِيَةٍ ۝٨
📖 Fassara Aya 8
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
وَجَاءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُ وَالْمُؤْتَفِكَاتُ بِالْخَاطِئَةِ ۝٩
📖 Fassara Aya 9
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
فَعَصَوْا رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً ۝١٠
📖 Fassara Aya 10
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
إِنَّا لَمَّا طَغَى الْمَاءُ حَمَلْنَاكُمْ فِي الْجَارِيَةِ ۝١١
📖 Fassara Aya 11
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَا أُذُنٌ وَاعِيَةٌ ۝١٢
📖 Fassara Aya 12
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
فَإِذَا نُفِخَ فِي الصُّورِ نَفْخَةٌ وَاحِدَةٌ ۝١٣
📖 Fassara Aya 13
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
وَحُمِلَتِ الْأَرْضُ وَالْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَاحِدَةً ۝١٤
📖 Fassara Aya 14
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ ۝١٥
📖 Fassara Aya 15
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
وَانشَقَّتِ السَّمَاءُ فَهِيَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ ۝١٦
📖 Fassara Aya 16
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
وَالْمَلَكُ عَلَىٰ أَرْجَائِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَانِيَةٌ ۝١٧
📖 Fassara Aya 17
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ ۝١٨
📖 Fassara Aya 18
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ فَيَقُولُ هَاؤُمُ اقْرَءُوا كِتَابِيَهْ ۝١٩
📖 Fassara Aya 19
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَاقٍ حِسَابِيَهْ ۝٢٠
📖 Fassara Aya 20
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ ۝٢١
📖 Fassara Aya 21
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ ۝٢٢
📖 Fassara Aya 22
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ ۝٢٣
📖 Fassara Aya 23
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا أَسْلَفْتُمْ فِي الْأَيَّامِ الْخَالِيَةِ ۝٢٤
📖 Fassara Aya 24
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِشِمَالِهِ فَيَقُولُ يَا لَيْتَنِي لَمْ أُوتَ كِتَابِيَهْ ۝٢٥
📖 Fassara Aya 25
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ ۝٢٦
📖 Fassara Aya 26
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
يَا لَيْتَهَا كَانَتِ الْقَاضِيَةَ ۝٢٧
📖 Fassara Aya 27
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
مَا أَغْنَىٰ عَنِّي مَالِيَهْ ۜ ۝٢٨
📖 Fassara Aya 28
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
هَلَكَ عَنِّي سُلْطَانِيَهْ ۝٢٩
📖 Fassara Aya 29
"Ĩkona ya ɓace mini!"
خُذُوهُ فَغُلُّوهُ ۝٣٠
📖 Fassara Aya 30
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
ثُمَّ الْجَحِيمَ صَلُّوهُ ۝٣١
📖 Fassara Aya 31
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
ثُمَّ فِي سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَاسْلُكُوهُ ۝٣٢
📖 Fassara Aya 32
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
إِنَّهُ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِاللَّهِ الْعَظِيمِ ۝٣٣
📖 Fassara Aya 33
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ ۝٣٤
📖 Fassara Aya 34
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
فَلَيْسَ لَهُ الْيَوْمَ هَاهُنَا حَمِيمٌ ۝٣٥
📖 Fassara Aya 35
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ ۝٣٦
📖 Fassara Aya 36
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
لَّا يَأْكُلُهُ إِلَّا الْخَاطِئُونَ ۝٣٧
📖 Fassara Aya 37
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
فَلَا أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ ۝٣٨
📖 Fassara Aya 38
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
وَمَا لَا تُبْصِرُونَ ۝٣٩
📖 Fassara Aya 39
Da abin da bã ku iya gani.
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ ۝٤٠
📖 Fassara Aya 40
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ ۝٤١
📖 Fassara Aya 41
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ ۝٤٢
📖 Fassara Aya 42
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَ ۝٤٣
📖 Fassara Aya 43
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ الْأَقَاوِيلِ ۝٤٤
📖 Fassara Aya 44
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِالْيَمِينِ ۝٤٥
📖 Fassara Aya 45
Dã Mun kãma shi da dãma.
ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ الْوَتِينَ ۝٤٦
📖 Fassara Aya 46
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَاجِزِينَ ۝٤٧
📖 Fassara Aya 47
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
وَإِنَّهُ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ ۝٤٨
📖 Fassara Aya 48
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ ۝٤٩
📖 Fassara Aya 49
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
وَإِنَّهُ لَحَسْرَةٌ عَلَى الْكَافِرِينَ ۝٥٠
📖 Fassara Aya 50
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
وَإِنَّهُ لَحَقُّ الْيَقِينِ ۝٥١
📖 Fassara Aya 51
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ ۝٥٢
📖 Fassara Aya 52
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
← 68 Al-Haqqah (69/114) 70 →
Karatu Surah Al-Haqqah Hausa – Fassara da Audio

69الحاقة Al-Haqqah 📚 52 Aya مكية



Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers