Surah An-Najm Larabci da Hausa

Karanta Surah An-Najm tare da cikakkiyar fassarar Hausa da sauti. Fassara aya bayan aya. (62 Aya — مكية). An-Najm Saurara, An-Najm Fassara, An-Najm mp3, An-Najm pdf.

Karanta da Saurara Surah An-Najm

🎧 Aya
M Mishary Rashid Alafasy
M Mahmoud Khalil Al-Husary
A Abdurrahman As-Sudais
M Mohamed Siddiq Al-Minshawi
A Abdul Basit Abdul Samad
A Ali Al-Hudhaify
A Ahmed ibn Ali al-Ajamy
A Abu Bakr Ash-Shaatree
M Muhammad Ayyoub
A Abdullah Basfar
A Abdullah Al-Juhani
M Maher Al Muaiqly
x1
وَالنَّجْمِ إِذَا هَوَىٰ ۝١
📖 Fassara Aya 1
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ ۝٢
📖 Fassara Aya 2
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
وَمَا يَنطِقُ عَنِ الْهَوَىٰ ۝٣
📖 Fassara Aya 3
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْيٌ يُوحَىٰ ۝٤
📖 Fassara Aya 4
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
عَلَّمَهُ شَدِيدُ الْقُوَىٰ ۝٥
📖 Fassara Aya 5
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.
ذُو مِرَّةٍ فَاسْتَوَىٰ ۝٦
📖 Fassara Aya 6
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
وَهُوَ بِالْأُفُقِ الْأَعْلَىٰ ۝٧
📖 Fassara Aya 7
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ ۝٨
📖 Fassara Aya 8
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ ۝٩
📖 Fassara Aya 9
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
فَأَوْحَىٰ إِلَىٰ عَبْدِهِ مَا أَوْحَىٰ ۝١٠
📖 Fassara Aya 10
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
مَا كَذَبَ الْفُؤَادُ مَا رَأَىٰ ۝١١
📖 Fassara Aya 11
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
أَفَتُمَارُونَهُ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ ۝١٢
📖 Fassara Aya 12
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
وَلَقَدْ رَآهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ ۝١٣
📖 Fassara Aya 13
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.
عِندَ سِدْرَةِ الْمُنتَهَىٰ ۝١٤
📖 Fassara Aya 14
A wurin da magaryar tuƙẽwa take.
عِندَهَا جَنَّةُ الْمَأْوَىٰ ۝١٥
📖 Fassara Aya 15
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
إِذْ يَغْشَى السِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ ۝١٦
📖 Fassara Aya 16
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
مَا زَاغَ الْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ ۝١٧
📖 Fassara Aya 17
Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ آيَاتِ رَبِّهِ الْكُبْرَىٰ ۝١٨
📖 Fassara Aya 18
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.
أَفَرَأَيْتُمُ اللَّاتَ وَالْعُزَّىٰ ۝١٩
📖 Fassara Aya 19
Shin, kun ga Lãta da uzza?
وَمَنَاةَ الثَّالِثَةَ الْأُخْرَىٰ ۝٢٠
📖 Fassara Aya 20
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
أَلَكُمُ الذَّكَرُ وَلَهُ الْأُنثَىٰ ۝٢١
📖 Fassara Aya 21
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
تِلْكَ إِذًا قِسْمَةٌ ضِيزَىٰ ۝٢٢
📖 Fassara Aya 22
Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.
إِنْ هِيَ إِلَّا أَسْمَاءٌ سَمَّيْتُمُوهَا أَنتُمْ وَآبَاؤُكُم مَّا أَنزَلَ اللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَانٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ وَمَا تَهْوَى الْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَاءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ الْهُدَىٰ ۝٢٣
📖 Fassara Aya 23
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
أَمْ لِلْإِنسَانِ مَا تَمَنَّىٰ ۝٢٤
📖 Fassara Aya 24
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
فَلِلَّهِ الْآخِرَةُ وَالْأُولَىٰ ۝٢٥
📖 Fassara Aya 25
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
۞ وَكَم مِّن مَّلَكٍ فِي السَّمَاوَاتِ لَا تُغْنِي شَفَاعَتُهُمْ شَيْئًا إِلَّا مِن بَعْدِ أَن يَأْذَنَ اللَّهُ لِمَن يَشَاءُ وَيَرْضَىٰ ۝٢٦
📖 Fassara Aya 26
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
إِنَّ الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِالْآخِرَةِ لَيُسَمُّونَ الْمَلَائِكَةَ تَسْمِيَةَ الْأُنثَىٰ ۝٢٧
📖 Fassara Aya 27
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
وَمَا لَهُم بِهِ مِنْ عِلْمٍ ۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ ۖ وَإِنَّ الظَّنَّ لَا يُغْنِي مِنَ الْحَقِّ شَيْئًا ۝٢٨
📖 Fassara Aya 28
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلَّا الْحَيَاةَ الدُّنْيَا ۝٢٩
📖 Fassara Aya 29
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
ذَٰلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ الْعِلْمِ ۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اهْتَدَىٰ ۝٣٠
📖 Fassara Aya 30
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
وَلِلَّهِ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ لِيَجْزِيَ الَّذِينَ أَسَاءُوا بِمَا عَمِلُوا وَيَجْزِيَ الَّذِينَ أَحْسَنُوا بِالْحُسْنَى ۝٣١
📖 Fassara Aya 31
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
الَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَائِرَ الْإِثْمِ وَالْفَوَاحِشَ إِلَّا اللَّمَمَ ۚ إِنَّ رَبَّكَ وَاسِعُ الْمَغْفِرَةِ ۚ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ الْأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌ فِي بُطُونِ أُمَّهَاتِكُمْ ۖ فَلَا تُزَكُّوا أَنفُسَكُمْ ۖ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اتَّقَىٰ ۝٣٢
📖 Fassara Aya 32
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
أَفَرَأَيْتَ الَّذِي تَوَلَّىٰ ۝٣٣
📖 Fassara Aya 33
Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?
وَأَعْطَىٰ قَلِيلًا وَأَكْدَىٰ ۝٣٤
📖 Fassara Aya 34
Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?
أَعِندَهُ عِلْمُ الْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىٰ ۝٣٥
📖 Fassara Aya 35
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ ۝٣٦
📖 Fassara Aya 36
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
وَإِبْرَاهِيمَ الَّذِي وَفَّىٰ ۝٣٧
📖 Fassara Aya 37
Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?
أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌ وِزْرَ أُخْرَىٰ ۝٣٨
📖 Fassara Aya 38
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
وَأَن لَّيْسَ لِلْإِنسَانِ إِلَّا مَا سَعَىٰ ۝٣٩
📖 Fassara Aya 39
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
وَأَنَّ سَعْيَهُ سَوْفَ يُرَىٰ ۝٤٠
📖 Fassara Aya 40
Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.
ثُمَّ يُجْزَاهُ الْجَزَاءَ الْأَوْفَىٰ ۝٤١
📖 Fassara Aya 41
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ الْمُنتَهَىٰ ۝٤٢
📖 Fassara Aya 42
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
وَأَنَّهُ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىٰ ۝٤٣
📖 Fassara Aya 43
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
وَأَنَّهُ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَا ۝٤٤
📖 Fassara Aya 44
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
وَأَنَّهُ خَلَقَ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ ۝٤٥
📖 Fassara Aya 45
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ ۝٤٦
📖 Fassara Aya 46
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
وَأَنَّ عَلَيْهِ النَّشْأَةَ الْأُخْرَىٰ ۝٤٧
📖 Fassara Aya 47
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
وَأَنَّهُ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ ۝٤٨
📖 Fassara Aya 48
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
وَأَنَّهُ هُوَ رَبُّ الشِّعْرَىٰ ۝٤٩
📖 Fassara Aya 49
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.
وَأَنَّهُ أَهْلَكَ عَادًا الْأُولَىٰ ۝٥٠
📖 Fassara Aya 50
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
وَثَمُودَ فَمَا أَبْقَىٰ ۝٥١
📖 Fassara Aya 51
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ ۝٥٢
📖 Fassara Aya 52
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
وَالْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىٰ ۝٥٣
📖 Fassara Aya 53
Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.
فَغَشَّاهَا مَا غَشَّىٰ ۝٥٤
📖 Fassara Aya 54
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ ۝٥٥
📖 Fassara Aya 55
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?
هَٰذَا نَذِيرٌ مِّنَ النُّذُرِ الْأُولَىٰ ۝٥٦
📖 Fassara Aya 56
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
أَزِفَتِ الْآزِفَةُ ۝٥٧
📖 Fassara Aya 57
Makusanciya fa, tã yi kusa.
لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ اللَّهِ كَاشِفَةٌ ۝٥٨
📖 Fassara Aya 58
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
أَفَمِنْ هَٰذَا الْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ ۝٥٩
📖 Fassara Aya 59
Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?
وَتَضْحَكُونَ وَلَا تَبْكُونَ ۝٦٠
📖 Fassara Aya 60
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
وَأَنتُمْ سَامِدُونَ ۝٦١
📖 Fassara Aya 61
Alhãli kunã mãsu wãsã?
فَاسْجُدُوا لِلَّهِ وَاعْبُدُوا ۩ ۝٦٢
📖 Fassara Aya 62
To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).
← 52 An-Najm (53/114) 54 →
Karatu Surah An-Najm Hausa – Fassara da Audio

53النجم An-Najm 📚 62 Aya مكية



Al-Kur'ani


Tuesday, August 18, 2026

Don't forget us in your sincere prayers