Surah An-Najm Larabci da Hausa
Karanta Surah An-Najm tare da cikakkiyar fassarar Hausa da sauti. Fassara aya bayan aya. (62 Aya — مكية). An-Najm Saurara, An-Najm Fassara, An-Najm mp3, An-Najm pdf.Karanta da Saurara Surah An-Najm
🎧 Aya
M
Mishary Rashid Alafasy
✓
Mishary Rashid Alafasy
✓
M
Mahmoud Khalil Al-Husary
✓
Mahmoud Khalil Al-Husary
✓
A
Abdurrahman As-Sudais
✓
Abdurrahman As-Sudais
✓
M
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
✓
Mohamed Siddiq Al-Minshawi
✓
A
Abdul Basit Abdul Samad
✓
Abdul Basit Abdul Samad
✓
A
Ali Al-Hudhaify
✓
Ali Al-Hudhaify
✓
A
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
✓
Ahmed ibn Ali al-Ajamy
✓
A
Abu Bakr Ash-Shaatree
✓
Abu Bakr Ash-Shaatree
✓
M
Muhammad Ayyoub
✓
Muhammad Ayyoub
✓
A
Abdullah Basfar
✓
Abdullah Basfar
✓
A
Abdullah Al-Juhani
✓
Abdullah Al-Juhani
✓
M
Maher Al Muaiqly
✓
Maher Al Muaiqly
✓
—
x1
مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ ٢
📖 Fassara
Aya 2
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْيٌ يُوحَىٰ ٤
📖 Fassara
Aya 4
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ ٩
📖 Fassara
Aya 9
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
فَأَوْحَىٰ إِلَىٰ عَبْدِهِ مَا أَوْحَىٰ ١٠
📖 Fassara
Aya 10
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
مَا كَذَبَ الْفُؤَادُ مَا رَأَىٰ ١١
📖 Fassara
Aya 11
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
أَفَتُمَارُونَهُ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ ١٢
📖 Fassara
Aya 12
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
وَلَقَدْ رَآهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ ١٣
📖 Fassara
Aya 13
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.
إِذْ يَغْشَى السِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ ١٦
📖 Fassara
Aya 16
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
مَا زَاغَ الْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ ١٧
📖 Fassara
Aya 17
Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ آيَاتِ رَبِّهِ الْكُبْرَىٰ ١٨
📖 Fassara
Aya 18
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.
أَلَكُمُ الذَّكَرُ وَلَهُ الْأُنثَىٰ ٢١
📖 Fassara
Aya 21
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
إِنْ هِيَ إِلَّا أَسْمَاءٌ سَمَّيْتُمُوهَا أَنتُمْ وَآبَاؤُكُم مَّا أَنزَلَ اللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَانٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ وَمَا تَهْوَى الْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَاءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ الْهُدَىٰ ٢٣
📖 Fassara
Aya 23
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
أَمْ لِلْإِنسَانِ مَا تَمَنَّىٰ ٢٤
📖 Fassara
Aya 24
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
فَلِلَّهِ الْآخِرَةُ وَالْأُولَىٰ ٢٥
📖 Fassara
Aya 25
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
۞ وَكَم مِّن مَّلَكٍ فِي السَّمَاوَاتِ لَا تُغْنِي شَفَاعَتُهُمْ شَيْئًا إِلَّا مِن بَعْدِ أَن يَأْذَنَ اللَّهُ لِمَن يَشَاءُ وَيَرْضَىٰ ٢٦
📖 Fassara
Aya 26
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
إِنَّ الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِالْآخِرَةِ لَيُسَمُّونَ الْمَلَائِكَةَ تَسْمِيَةَ الْأُنثَىٰ ٢٧
📖 Fassara
Aya 27
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
وَمَا لَهُم بِهِ مِنْ عِلْمٍ ۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ ۖ وَإِنَّ الظَّنَّ لَا يُغْنِي مِنَ الْحَقِّ شَيْئًا ٢٨
📖 Fassara
Aya 28
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلَّا الْحَيَاةَ الدُّنْيَا ٢٩
📖 Fassara
Aya 29
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
ذَٰلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ الْعِلْمِ ۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اهْتَدَىٰ ٣٠
📖 Fassara
Aya 30
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
وَلِلَّهِ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ لِيَجْزِيَ الَّذِينَ أَسَاءُوا بِمَا عَمِلُوا وَيَجْزِيَ الَّذِينَ أَحْسَنُوا بِالْحُسْنَى ٣١
📖 Fassara
Aya 31
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
الَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَائِرَ الْإِثْمِ وَالْفَوَاحِشَ إِلَّا اللَّمَمَ ۚ إِنَّ رَبَّكَ وَاسِعُ الْمَغْفِرَةِ ۚ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ الْأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌ فِي بُطُونِ أُمَّهَاتِكُمْ ۖ فَلَا تُزَكُّوا أَنفُسَكُمْ ۖ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اتَّقَىٰ ٣٢
📖 Fassara
Aya 32
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
أَعِندَهُ عِلْمُ الْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىٰ ٣٥
📖 Fassara
Aya 35
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ ٣٦
📖 Fassara
Aya 36
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌ وِزْرَ أُخْرَىٰ ٣٨
📖 Fassara
Aya 38
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
وَأَن لَّيْسَ لِلْإِنسَانِ إِلَّا مَا سَعَىٰ ٣٩
📖 Fassara
Aya 39
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
ثُمَّ يُجْزَاهُ الْجَزَاءَ الْأَوْفَىٰ ٤١
📖 Fassara
Aya 41
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ الْمُنتَهَىٰ ٤٢
📖 Fassara
Aya 42
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
وَأَنَّهُ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىٰ ٤٣
📖 Fassara
Aya 43
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
وَأَنَّهُ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَا ٤٤
📖 Fassara
Aya 44
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
وَأَنَّهُ خَلَقَ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ ٤٥
📖 Fassara
Aya 45
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ ٤٦
📖 Fassara
Aya 46
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
وَأَنَّ عَلَيْهِ النَّشْأَةَ الْأُخْرَىٰ ٤٧
📖 Fassara
Aya 47
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
وَأَنَّهُ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ ٤٨
📖 Fassara
Aya 48
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
وَأَنَّهُ أَهْلَكَ عَادًا الْأُولَىٰ ٥٠
📖 Fassara
Aya 50
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ ٥٢
📖 Fassara
Aya 52
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ ٥٥
📖 Fassara
Aya 55
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?
هَٰذَا نَذِيرٌ مِّنَ النُّذُرِ الْأُولَىٰ ٥٦
📖 Fassara
Aya 56
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ اللَّهِ كَاشِفَةٌ ٥٨
📖 Fassara
Aya 58
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
أَفَمِنْ هَٰذَا الْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ ٥٩
📖 Fassara
Aya 59
Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?
فَاسْجُدُوا لِلَّهِ وَاعْبُدُوا ۩ ٦٢
📖 Fassara
Aya 62
To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).
Karatu Surah An-Najm Hausa – Fassara da Audio
Al-Kur'ani
Tuesday, August 18, 2026
Don't forget us in your sincere prayers

