سوره واقعه به زبان هَوُسَ

  1. گوش دادن به سوره
  2. سورهای دیگر
  3. ترجمه سوره
قرآن کریم | ترجمه معانی قرآن | زبان هَوُسَ | سوره واقعه | الواقعة - تعداد آیات آن 96 - شماره سوره در مصحف: 56 - معنی سوره به انگلیسی: The Inevitable, The Event.

إِذَا وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ(1)

 Idan mai aukuwa ta auku.

لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ(2)

 Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.

خَافِضَةٌ رَّافِعَةٌ(3)

 (Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.

إِذَا رُجَّتِ الْأَرْضُ رَجًّا(4)

 Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.

وَبُسَّتِ الْجِبَالُ بَسًّا(5)

 Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.

فَكَانَتْ هَبَاءً مُّنبَثًّا(6)

 Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.

وَكُنتُمْ أَزْوَاجًا ثَلَاثَةً(7)

 Kuma kun kasance nau'i uku.

فَأَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ مَا أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ(8)

 Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

وَأَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ مَا أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ(9)

 Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?

وَالسَّابِقُونَ السَّابِقُونَ(10)

 Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,

أُولَٰئِكَ الْمُقَرَّبُونَ(11)

 Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.

فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ(12)

 A ckin Aljannar ni'ima.

ثُلَّةٌ مِّنَ الْأَوَّلِينَ(13)

 Jama'a ne daga mutãnen farko.

وَقَلِيلٌ مِّنَ الْآخِرِينَ(14)

 Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.

عَلَىٰ سُرُرٍ مَّوْضُونَةٍ(15)

 (Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.

مُّتَّكِئِينَ عَلَيْهَا مُتَقَابِلِينَ(16)

 Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.

يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَانٌ مُّخَلَّدُونَ(17)

 Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.

بِأَكْوَابٍ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ(18)

 Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.

لَّا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنزِفُونَ(19)

 Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.

وَفَاكِهَةٍ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ(20)

 Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.

وَلَحْمِ طَيْرٍ مِّمَّا يَشْتَهُونَ(21)

 Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.

وَحُورٌ عِينٌ(22)

 Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.

كَأَمْثَالِ اللُّؤْلُؤِ الْمَكْنُونِ(23)

 Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.

جَزَاءً بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ(24)

 A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.

لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا تَأْثِيمًا(25)

 Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.

إِلَّا قِيلًا سَلَامًا سَلَامًا(26)

 Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.

وَأَصْحَابُ الْيَمِينِ مَا أَصْحَابُ الْيَمِينِ(27)

 Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

فِي سِدْرٍ مَّخْضُودٍ(28)

 (Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.

وَطَلْحٍ مَّنضُودٍ(29)

 Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.

وَظِلٍّ مَّمْدُودٍ(30)

 Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.

وَمَاءٍ مَّسْكُوبٍ(31)

 Da wani ruwa mai gudãna.

وَفَاكِهَةٍ كَثِيرَةٍ(32)

 Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.

لَّا مَقْطُوعَةٍ وَلَا مَمْنُوعَةٍ(33)

 Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.

وَفُرُشٍ مَّرْفُوعَةٍ(34)

 Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.

إِنَّا أَنشَأْنَاهُنَّ إِنشَاءً(35)

 Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.

فَجَعَلْنَاهُنَّ أَبْكَارًا(36)

 Sa'an nan Muka sanya su budurwai.

عُرُبًا أَتْرَابًا(37)

 Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.

لِّأَصْحَابِ الْيَمِينِ(38)

 Ga mazõwa dãma.

ثُلَّةٌ مِّنَ الْأَوَّلِينَ(39)

 Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.

وَثُلَّةٌ مِّنَ الْآخِرِينَ(40)

 Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.

وَأَصْحَابُ الشِّمَالِ مَا أَصْحَابُ الشِّمَالِ(41)

 Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?

فِي سَمُومٍ وَحَمِيمٍ(42)

 Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

وَظِلٍّ مِّن يَحْمُومٍ(43)

 Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.

لَّا بَارِدٍ وَلَا كَرِيمٍ(44)

 Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.

إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ(45)

 Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.

وَكَانُوا يُصِرُّونَ عَلَى الْحِنثِ الْعَظِيمِ(46)

 Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

وَكَانُوا يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ(47)

 Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"

أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ(48)

 "Shin, kuma da ubanninmu na farko?"

قُلْ إِنَّ الْأَوَّلِينَ وَالْآخِرِينَ(49)

 Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."

لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَاتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ(50)

 "Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."

ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا الضَّالُّونَ الْمُكَذِّبُونَ(51)

 "Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

لَآكِلُونَ مِن شَجَرٍ مِّن زَقُّومٍ(52)

 "Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ(53)

 "Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

فَشَارِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ الْحَمِيمِ(54)

 "Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

فَشَارِبُونَ شُرْبَ الْهِيمِ(55)

 "Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

هَٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ الدِّينِ(56)

 Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

نَحْنُ خَلَقْنَاكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ(57)

 Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

أَفَرَأَيْتُم مَّا تُمْنُونَ(58)

 Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

أَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُ أَمْ نَحْنُ الْخَالِقُونَ(59)

 Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ الْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ(60)

 Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,

عَلَىٰ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَالَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِي مَا لَا تَعْلَمُونَ(61)

 A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ النَّشْأَةَ الْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ(62)

 Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

أَفَرَأَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ(63)

 Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

أَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُ أَمْ نَحْنُ الزَّارِعُونَ(64)

 Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

لَوْ نَشَاءُ لَجَعَلْنَاهُ حُطَامًا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ(65)

 Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

إِنَّا لَمُغْرَمُونَ(66)

 (Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ(67)

 "Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

أَفَرَأَيْتُمُ الْمَاءَ الَّذِي تَشْرَبُونَ(68)

 Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

أَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ الْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ الْمُنزِلُونَ(69)

 Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

لَوْ نَشَاءُ جَعَلْنَاهُ أُجَاجًا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ(70)

 Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

أَفَرَأَيْتُمُ النَّارَ الَّتِي تُورُونَ(71)

 Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

أَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَا أَمْ نَحْنُ الْمُنشِئُونَ(72)

 Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

نَحْنُ جَعَلْنَاهَا تَذْكِرَةً وَمَتَاعًا لِّلْمُقْوِينَ(73)

 Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ(74)

 Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

۞ فَلَا أُقْسِمُ بِمَوَاقِعِ النُّجُومِ(75)

 To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.

وَإِنَّهُ لَقَسَمٌ لَّوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ(76)

 Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.

إِنَّهُ لَقُرْآنٌ كَرِيمٌ(77)

 Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.

فِي كِتَابٍ مَّكْنُونٍ(78)

 A cikin wani littafi tsararre.

لَّا يَمَسُّهُ إِلَّا الْمُطَهَّرُونَ(79)

 Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.

تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَ(80)

 Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.

أَفَبِهَٰذَا الْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ(81)

 Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?

وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ(82)

 Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?

فَلَوْلَا إِذَا بَلَغَتِ الْحُلْقُومَ(83)

 To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).

وَأَنتُمْ حِينَئِذٍ تَنظُرُونَ(84)

 Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.

وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ(85)

 Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.

فَلَوْلَا إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ(86)

 To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?

تَرْجِعُونَهَا إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ(87)

 Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.

فَأَمَّا إِن كَانَ مِنَ الْمُقَرَّبِينَ(88)

 To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,

فَرَوْحٌ وَرَيْحَانٌ وَجَنَّتُ نَعِيمٍ(89)

 Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.

وَأَمَّا إِن كَانَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ(90)

 Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,

فَسَلَامٌ لَّكَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ(91)

 Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.

وَأَمَّا إِن كَانَ مِنَ الْمُكَذِّبِينَ الضَّالِّينَ(92)

 Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,

فَنُزُلٌ مِّنْ حَمِيمٍ(93)

 Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.

وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ(94)

 Da ƙõnuwa da Jahĩm,

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ الْيَقِينِ(95)

 Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.

فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ(96)

 Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.


سورهای بیشتر به زبان هَوُسَ:

سوره البقره آل عمران سوره نساء
سوره مائده سوره يوسف سوره ابراهيم
سوره حجر سوره کهف سوره مریم
سوره حج سوره قصص سوره عنکبوت
سوره سجده سوره یس سوره دخان
سوره فتح سوره حجرات سوره ق
سوره نجم سوره رحمن سوره واقعه
سوره حشر سوره ملک سوره حاقه
سوره انشقاق سوره أعلى سوره غاشية

دانلود سوره واقعه با صدای معروف‌ترین قراء:

انتخاب خواننده برای گوش دادن و دانلود کامل سوره واقعه با کیفیت بالا.
سوره واقعه را با صدای احمد العجمی
أحمد العجمي
سوره واقعه را با صدای ابراهيم الاخضر
ابراهيم الاخضر
سوره واقعه را با صدای بندر بليلة
بندر بليلة
سوره واقعه را با صدای خالد الجليل
خالد الجليل
سوره واقعه را با صدای حاتم فريد الواعر
حاتم فريد الواعر
سوره واقعه را با صدای خليفة الطنيجي
خليفة الطنيجي
سوره واقعه را با صدای سعد الغامدي
سعد الغامدي
سوره واقعه را با صدای سعود الشريم
سعود الشريم
سوره واقعه را با صدای الشاطري
الشاطري
سوره واقعه را با صدای صلاح ابوخاطر
صلاح بوخاطر
سوره واقعه را با صدای عبد الباسط عبد الصمد
عبد الباسط
سوره واقعه را با صدای عبد الرحمن العوسي
عبدالرحمن العوسي
سوره واقعه را با صدای عبد الرشيد صوفي
عبد الرشيد صوفي
سوره واقعه را با صدای عبد العزيز الزهراني
عبدالعزيز الزهراني
سوره واقعه را با صدای عبد الله بصفر
عبد الله بصفر
سوره واقعه را با صدای عبد الله عواد الجهني
عبد الله الجهني
سوره واقعه را با صدای علي الحذيفي
علي الحذيفي
سوره واقعه را با صدای علي جابر
علي جابر
سوره واقعه را با صدای غسان الشوربجي
غسان الشوربجي
سوره واقعه را با صدای فارس عباد
فارس عباد
سوره واقعه را با صدای ماهر المعيقلي
ماهر المعيقلي
سوره واقعه را با صدای محمد أيوب
محمد أيوب
سوره واقعه را با صدای محمد المحيسني
محمد المحيسني
سوره واقعه را با صدای محمد جبريل
محمد جبريل
سوره واقعه را با صدای محمد صديق المنشاوي
المنشاوي
سوره واقعه را با صدای الحصري
الحصري
سوره واقعه را با صدای العفاسي
مشاري العفاسي
سوره واقعه را با صدای ناصر القطامي
ناصر القطامي
سوره واقعه را با صدای وديع اليمني
وديع اليمني
سوره واقعه را با صدای ياسر الدوسري
ياسر الدوسري


Sunday, May 12, 2024

به قرآن کریم چنگ بزنید